• English
  • Business News
Wednesday, October 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matatar Dangote Ta Amince Da Ƙudurori 5, PENGASSAN Za Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Da Ta Tsunduma

by Sulaiman
4 hours ago
in Manyan Labarai
0
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alamu masu ƙarfi a safiyar yau Laraba na nuna cewa kungiyar manyan ma’aikatan man fetur da iskar gas ta Nijeriya (PENGASSAN) na iya dakatar da yajin aikin da take yi biyo bayan sulhu da gwamnatin tarayya ta kulla da mahukuntan matatar man Dangote.

 

Bayan doguwar tattaunawa a taron sasantawa da aka gudanar a Abuja a ranakun 29 da 30 ga watan Satumban 2025, bangarorin biyu sun amince da kuduri mai dauke da abubuwa biyar.

  • Gwamnatin Gombe Ta Haramta Kiwon Dare, Ta Taƙaita Zirga-zirgar Makiyaya Kafin Fara Girbi A Jihar
  • Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Kimiyya Da Fasaha

Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Mohammed Maigari Dingyadi, a wata sanarwa bayan taron, ya tabbatar da cewa, shiga kungiya, haƙƙi ne na ma’aikata bisa ƙa’ida a ƙarƙashin dokokin mulkin Nijeriya, wanda dole ne a kiyaye.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Gombe Ta Haramta Kiwon Dare, Ta Taƙaita Zirga-zirgar Makiyaya Kafin Fara Girbi A Jihar

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Biyan Ƙarin ₦32,000 Ga ‘Yan Fansho

An kuma amince da cewa ma’aikatan da aka kora za a mayar da su kan ayyukan su cikin wasu kamfanoni na rukunin Dangote ba tare da sun yi asarar albashi ba, kuma babu wani ma’aikaci da za a ci zarafinsa saboda rawar da ya taka a wannan taƙaddamar.

 

 

An cimma matsayar ne a gaban manyan jami’an gwamnati da suka hada da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, ministan kudi kuma mai kula da tattalin arziki, ministan kasafin kudi da tsare-tsare, karamin ministan albarkatun man fetur (Gas) da shugabannin NMDPRA da NUPRC, da wakilan kamfanin man fetur na kasa (NNPCL).

 

Haka kuma shugabannin kungiyar ‘yan kasuwa (TUC) sun halarci tattaunawar tare da shugabannin kungiyar ta PENGASSAN da kuma mahukuntan matatar Dangote.

 

Idan dai za a iya tunawa dai rikicin ya samo asali ne bayan da matatar man ta Dangote ta kori mambobin kungiyar ta PENGASSAN sama da 800, lamarin da ya sa kungiyar ta fitar da umarnin dakatar da samar da iskar gas ga matatar ta kuma janye ayyukanta a fadin kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Gombe Ta Haramta Kiwon Dare, Ta Taƙaita Zirga-zirgar Makiyaya Kafin Fara Girbi A Jihar

Next Post

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

Related

Gwamnatin Gombe Ta Haramta Kiwon Dare, Ta Taƙaita Zirga-zirgar Makiyaya Kafin Fara Girbi A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnatin Gombe Ta Haramta Kiwon Dare, Ta Taƙaita Zirga-zirgar Makiyaya Kafin Fara Girbi A Jihar

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Biyan Ƙarin ₦32,000 Ga ‘Yan Fansho
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Biyan Ƙarin ₦32,000 Ga ‘Yan Fansho

20 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Ta Sace Kwamishinan Zaɓe A Neja, Tsohon Shugaban SUBEB, Da Wasu

1 day ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Laraba A Matsayin Hutu Don Bikin Ranar Samun ’Yancin Kai
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Laraba A Matsayin Hutu Don Bikin Ranar Samun ’Yancin Kai

1 day ago
Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Janye Yajin Aikin Watanni Takwas Da Take Yi 
Manyan Labarai

ASUU Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwanaki 14 Don Biyan Buƙatunta

1 day ago
Gwamnatin Tarayya Ta Soke Bikin Faretin Ranar Samun ’Yancin Kai
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Soke Bikin Faretin Ranar Samun ’Yancin Kai

1 day ago
Next Post
Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

LABARAI MASU NASABA

NNPCL Ya Ƙulla Sabuwar Yarjejeniya Ta Samar Da Ɗanyen Mai Na Shekaru Biyu Da Matatar Dangote

NNPCL Ya Ƙulla Sabuwar Yarjejeniya Ta Samar Da Ɗanyen Mai Na Shekaru Biyu Da Matatar Dangote

October 1, 2025
Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

October 1, 2025
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Matatar Dangote Ta Amince Da Ƙudurori 5, PENGASSAN Za Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Da Ta Tsunduma

October 1, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Haramta Kiwon Dare, Ta Taƙaita Zirga-zirgar Makiyaya Kafin Fara Girbi A Jihar

Gwamnatin Gombe Ta Haramta Kiwon Dare, Ta Taƙaita Zirga-zirgar Makiyaya Kafin Fara Girbi A Jihar

October 1, 2025
Ci Gaban Sin Mai Inganci Ya Samar Da Damammaki Ga Duniya

Ci Gaban Sin Mai Inganci Ya Samar Da Damammaki Ga Duniya

September 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Kundi Mai Kunshe Da Matsayinta Dangane Da Kudurin MDD Mai Lamba 2758

Sin Ta Fitar Da Kundi Mai Kunshe Da Matsayinta Dangane Da Kudurin MDD Mai Lamba 2758

September 30, 2025
Matatar Ɗangote Ta Zargi Ƙungiyar PENGASSAN Da Yi Wa Al’ummar Nijeriya Zagon Ƙasa

Matatar Ɗangote Ta Zargi Ƙungiyar PENGASSAN Da Yi Wa Al’ummar Nijeriya Zagon Ƙasa

September 30, 2025
Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Kimiyya Da Fasaha

Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Kimiyya Da Fasaha

September 30, 2025
Obasanjo

Nijeriya Ba Ta Da Sarƙaƙiyar Jagoranci Idan Ta Samu Shugabanni Masu Gaskiya – Obasanjo 

September 30, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Wanzar Da Zamanantarwa Irin Ta Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Wanzar Da Zamanantarwa Irin Ta Sin

September 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.