ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Kimiyya Da Fasaha

by Sulaiman
8 months ago
Sin

A baya-bayan nan ne ministan ma’aikatar kimiyya da fasaha ta kasar Sin Yin Hejun da kwamishinan AU mai lura da harkokin ilimi, kimiyya da kirkire-kirkiren fasaha, Gaspard Banyankimbona, suka sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna, a madadin gwamnatin jamhuriyar jama’ar kasar Sin da kungiyar AU, dangane da hadin gwiwar raya bangaren kimiyya da fasaha.

Karkashin wannan yarjejeniya, sassan biyu za su yi hadin kai wajen aiwatar da bincike, da gina dandalin hadin gwiwa na raya fasahohi, da aiwatar da musayar kwarewar fasahohi, da kirkire-kirkire da sana’o’i da sauransu.

Ina matukar taya nahiyar Afrika murna domin wannan abun farin ciki ne gare ta, ganin cewa idan batu ake na kimiyya da fasahar zamani, to dole ne a kira kasar Sin saboda dimbin ci gaban da ta samu da ma yadda take mayar da hankali wajen bincike da kirkire-kirkire da kuma yadda a kusan kullum, masana a kasar ke bullo da sabbin abubuwa na kimiyya da fasaha. Baya ga haka, babu mafi dacewa da ya kamata nahiyar Afrika ta hada gwiwa da ita a wannan fanni da ya wuce kasar Sin, duba da muradinta na ganin an ci gaba tare, an samu moriya tare da kuma yadda take taimakawa ba tare da rufa-rufa ko gindaya sharadi ko ma katsalandan cikin harkokin kasashe ba.

ADVERTISEMENT

Kasar Sin ta ciri tuta idan ana batu na kimiyya da fasaha. Cikin mizanin kirkire-kirkire na duniya da hukumar kula da hakkin mallaka ta duniya WIPO ta fitar a baya-bayan nan, a karon farko kasar Sin ta shiga jerin kasashe 10 dake kan gaba a fannin kirkire-kirkire, lamarin da ya tabbatar da ci gaban da kasar ke samu da kuma nuna kwalliya ta biyan kudin sabulu daga jajircewarta da manufofi da dimbin jarin da take zubawa bangaren.

Yayin da kasashe masu tasowa suka kasance koma baya, ci gaban kasar Sin zaburarwa ce a gare su cewa, su ma za su iya dogaro da karfinsu, kuma su samu ci gaba. Haka kuma, taimakonta gare su, ba shakka zai taka rawa wajen daga matsayinsu da kwarewarsu a fannin kimiyya da fasaha. Kamar yadda kullum nake fada, ci gaban kasar Sin, ci gaba ne ga kasashenmu na nahiyar Afrika domin duk wata nasara da ta samu, tana son su ma su samu. Don haka, ina ganin wannan hadin gwiwa da AU ta yi da Sin, dama ce ga kasashen Afrika ta kara karfinsu da kwarewa a bangaren ta yadda za su samu ci gaba kuma al’ummominsu su amfana.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Matatar Ɗangote Ta Zargi Ƙungiyar PENGASSAN Da Yi Wa Al’ummar Nijeriya Zagon Ƙasa

Matatar Ɗangote Ta Zargi Ƙungiyar PENGASSAN Da Yi Wa Al'ummar Nijeriya Zagon Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.