• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
6 hours ago
TRCN

Hukumar Rajistar Malamai ta Nijeriya (TRCN) ta nuna damuwa kan yawaitar malaman da ba su cancanta ba a kasar, inda ta bayyana hakan a matsayin babban dalilin raguwar ingancin ilimi.

 

Babban Daraktan TRCN, Dr. Ronke Soyombo ce ta bayyana hakan a ranar Litinin yayin bayyanarta a shirin ‘The Morning Brief na tashar Channels Telebision, a lokacin bikin Ranar Malamai ta Duniya ta 2025, mai taken “Sake Tsara Koyarwa a Matsayin Sana’a ta Hadin Kai.”

 

Dr. Soyombo ta yi bakin ciki da cewa mutane da yawa da ke koyarwa a makarantu a fadin Nijeriya ba su da cancantar da ake bukata don gudanar da aikinsu yadda ya kamata, abin da ya fi shafar makarantu masu zaman kansu.

LABARAI MASU NASABA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

 

“Akwai da yawa malamai marasa cancanta a cikin aikin. Muna da wadanda ke koyarwa a ajujuwa amma ba su da takardun shaidar koyarwa, musamman a makarantu masu zaman kansu,” in ji ta.

 

Ta bayyana cewa, yayin da wasu mutane ke da sha’awar koyarwa da gaske, rashin horo na hukuma ya hana su shiga aikin koyarwa.

 

Dr. Soyombo ta bayyana cewa TRCN a halin yanzu na da malamai masu rijista kusan miliyan 1.4, tare da shirin kara wannan adadi zuwa miliyan 20 cikin shekaru biyu masu zuwa ta hanyar dijital da saurin rajista.

 

“Mun zamanantar da tsarinmu domin mutane da yawa su sami damar yin rijista,” in ji ta. “Kowane malami yana da bai wa ta musamman wadda ta bambanta da ta wani. Amma abin da muke kokarin yi domin inganta ilimi shi ne kowa ya zo tare da tsarinsa na darussa.”

 

“Za ku iya zama malamai uku da ke koyarwa ga rukuni guda na dalibai, kuma idan kuka zo tsara darusa tare tabbas za ku samar da wani abu mai dimbin fa’ida fiye da lokacin da kake aiki kai kadai.”

 

“Babu shakka akwai karancin malamai, don haka abin da muke yi tare da wannan gwamnati shi ne gaggauta shirin Diploma na Kwarewa a Fannin Ilimi (PDE). Ga wadanda ba su da shi, yanzu lokaci ne da za su iya samun dama. Muna gaggauta kwas din zuwa watanni shida ga malamai masu kwarewa, domin da zaran sun kammala, za su sami kwarewa. Wannan zai sa mu samu isassun ma’aikata a fannin koyarwa.”

 

“Abin da TRCN ke yi kuma shi ne duba yadda za mu inganta malamai. Haka kuma, muna tallafa musu da kayan aiki a cikin ajujuwa, domin wasu malamai suna da kwarewa sosai kuma suna neman yadda za su tsara darussa don tallafawa sauran malamai, kuma hakan zai karfafa wasu su shigo,” in ji ta.

 

A halin da ake ciki, Uwargidan Shugaban Kasa, Sanata Oluremi Tinubu, a cikin sakonta na Ranar Malamai ta Duniya, ta yaba wa malamai kan gudummawar da ba za a iya misaltawa ba wajen gina kasa, sannan ta yi kira ga kokari na musamman don magance karancin malamai a duniya.

 

Tinubu ta bayyana malamai a matsayin “jarumai, masu tsara tunani, da jagorantar karni,” inda ya jaddada cewa inganta walwalarsu da ci gaban kwarewarsu na aiki shi ne mabudin karfafa tsarin ilimi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya
Labarai

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Nijeriya
Labarai

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Next Post
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

LABARAI MASU NASABA

Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.