ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

by Shehu Yahaya and Sulaiman
8 months ago
Kwastam

Guguwar ritaya mai karfi za ta girgiza Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS) a shekarar 2026, yayin da jami’ai 825 za su bar aiki bisa ka’idar ritaya, kamar yadda jaridar LEADERSHIP Hausa ta gano.

 

A watan Agusta na shekarar 2025 rahotanni sun bayyana cewa akalla jami’ai 791 na hukumar za su yi ritaya a shekarar 2026, Sai dai kamar yadda aka zata, adadin ya karu zuwa 825, karin mutum 34, bisa jerin sunayen da hukumar ta sanya suna: “Jerin karshe Na Jami’ai Da Ma’aikata Don Ritaya A Shekarar 2026.

ADVERTISEMENT
  • Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa
  • Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Wannan adadi ya zama babba idan aka kwatanta da yawan ma’aikatan hukumar gaba daya da ke kusan 18,000 a fadin kasar nan wanda ya yi kasa sosai da 30,000 da Majalisar Tarayya ta tsara a matsayin adadin da hukumar ke bukata.

 

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Wannan lamari ya haifar da tambaya kan yiwuwar dorewar shirin sauye-sauye da na zamani da ake gudanarwa a karkashin jagorancin Babban Kwanturola Janar, Adewale Adeniyi.

 

Adewale Adeniyi, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kara wa wa’adin mulki na shekara guda, shima zai yi ritaya daga hukumar a watan Agusta, 2026.

 

A halin yanzu, za a dauki babban mataki kafin a cike gibin ma’aikata da ake bukata a hukumar kwastam, musamman idan aka yi la’akari da cewa jami’ai 825 za su bar aiki ba tare da sabon daukar ma’aikata ba.

 

Binciken da leadership Hausa ta gudanar ya gano cewa ritayar ta shafi kowane mataki a hukumar daga manyan shugabanni, zuwa matsakaita, har da kananan jami’ai.

 

Daga cikin jami’ai 825 da za su yi ritaya saboda shekaru 60 da suka kai ko kuma shekaru 35 na aiki:

 

5 suna da mukamin mataimakan kwanturola na kasa wato (DCG) sai wasu kananan mataimaka Kwanturola na kasa (ACG) su 13 sai kuma Kwanturololi ( CAC) guda 53 da mataimakanau (DC) guda 51 kananan mataimaka Kwanturola ( AC) guda 46.

 

Sauran sune ; masu mukaman (CSC) guda 61 sai ( SC) Guda 226 da ( DSC) su 285 sai (ASC I) 64 da (ASC II) su 10 (IC), su 8 (CA I) guda 1 sai (CA II) su 2 Jami’an mataimaka Kwanturola Janar ( DCG) guda biyar da ritayar ta shafa su ne: Mista C.K. Niagwan da K.I. Adeola da kuma Mista S. Chiroma; Mr. G.M. Omale; da Mista A. Nnadi.

 

Kananan Jami’an mataimaka Kwanturola Janar (ACG) guda goma sha uku (13) da abin ya shafa su ne: K.C. Egwuh, M.S. Yusuf, da Z.M. Gaji da N.P. Umoh da O.A. Adebakin da kuma T. Bomodi da B.O. Olomu, O.P. Olaniyan, I.K. Oladeji, K. Mohammed, O.A. Adebakin, da B. Mohammed, da C.C. Dim.

 

Daga cikin Kwanturololi da za su yi ritaya a 2026, akwai: D. Abubakar, da O.Y. Shuaibu, F.A. Bodunde da P.C. Chibuoke, da kuma O.O. Akingbade, da A. Salihu, da wasu da dama.

 

A matsayin shiri kafin ranar ritayar 2026, Hedikwatar Hukumar Kwastam da ke Abuja ta bayar da umarni ga dukkan jami’an da abin ya shafa su fara shirye-shiryen barin aiki kamin ranar ta isko su.

 

Hakazalika, An umurce su da su mika sanarwar izinin hutu na watanni uku kafin ritaya ga Babban Kwanturola Janar na Kwastam (CGC).

 

A cikin takardar da wakilinmu ya gani mai taken “Jerin karshe Na Jami’ai da Ma’aikata Don Ritaya A Shekarar 2026”, wacce aka fitar ranar 19 ga Satumba, 2025, kuma Kwanturola A.A. Bazuaye ya sanya hannu a madadin DCG na Sashen Albarkatun Dan Adam (HR), an bukaci jami’an da abin ya shafa da su bi doka da tsari.

 

Kamar yadda takardar ta ce: “A bisa Dokar Aikin Gwamnati (PSR No. 100238) da kuma Sanarwar Gwamnati mai lamba 36216/S.1/D/T: CR1/2001/5 na 20/3/2001, dukkan jami’an da suka cika shekarun ritaya a 2026 za su bar aiki kuma su tafi hutu na watanni uku kafin ranar da ritayar za ta fara aiki.”

 

Haka kuma, an umurci dukkan jami’an da abin ya shafa su tabbatar da bin umarnin, tare da tura takardar sanarwar hutun ritayarsu ga Babban Kwanturola Janar yadda ya dace.

 

Takardar ta kuma bukaci Koordinetocin Yankuna da Kwamandojin Yankuna su sanar da duk jami’an da abin ya shafa a yankunansu.

 

Da wannan yawan ma’aikata da za su bar aiki a 2026, har yanzu ana cikin tunanin irin dabarar da shugabancin kwastam zai yi amfani da ita don cike gibin da zai biyo baya, tare da tabbatar da ci gaba da sabbin domin gudanar da ayyukan hukumar.

Kwastam
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
Kwastam
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Labarai

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Next Post
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari'a Da Inganta Shugabanci A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.