• English
  • Business News
Sunday, October 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya?

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
5 hours ago
Afirka

Amurka da China da Rasha ba su cika haduwa a teburi daya ba, duk da cewa akwai wasu abubuwan da dama da suke haduwa a kai.

Dukkansu sun amince nahiyar Afirka ta samu kujerar dindindin a kwamitin tsaro. Amma shin me ya sa har yanzu ba a tabbatar ba?

A kwamitin tsaro na MDD, akwai kasashe biyar masu kujerar dindindin wato China da Rasha da Faransa da Birtaniya da Amurka, wadanda ake kira da P5. Su kadai ne mambobin da suke da damar hawa kujerar na-ki.

Sauran kasashen Majalisar Dinkin Duniya suna samun damar zama a kwamitin tsaron ne lokaci bayan lokaci, amma ba su da karfin ikon hawa kujerar na-ki.

‘Tabbatar da tsaron Afirka dole ne’

LABARAI MASU NASABA

Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor

Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya ce akwai bukatar gyara.

“Ba za a taba yi iya samar da tsaro a duniya ba, ba tare da tabbatar da tsaron Afirka ba,” in ji shi.

“Bai dace ba a ce kwamitin tsaro na duniya babu wakilcin nahiyar da ke da sama da mutum biliyan 1, wadda kuma mutanenta ke kara hayayyafa, kuma yanzu haka nahiyar ce ke da kashi 28 na kasashen Majalisar Dinkin Duniya.”

Kungiyar Tarayyar Afirka ta bukaci “akalla kujera biyu ta dindindin” da karfin ikon hawa kujerar na-ki, da kuma karin kujera biyar da ba na dindindin ba.

Amma duk da cewa yawancin kasashen majalisar sun amince akwai bukatar Afirka ta samu damar, masanin diflomasiyya a majalisar, Richard Gowan ya ce ya ce ba su shirya ba.

Gowan ya ce gwamnatin Amurka a karkashin Biden ta bayyana goyon bayanta kan yunkurin Afirka na samun kujera biyu, amma ba tare da karfin kujerar na-ki ba. Amma ya ce Trump ya nuna cewa ya fi son kwamitin a yadda yake, kuma ba ya so kasashe masu karfin hawa kujerar na-ki su yi yawa.

 

Wadanne kasashe daga Afirka?

Wata babbar matsalar da ke ci wa Afirka tuwo a kwarya ita ce shin wace kasa ce ta fi cancantar darewa kujerar guda daya ko biyu a kwamitin?

Kasashen da ake bayyanawa daga Afirka su ne Afirka ta Kudu da Nijeriya da Kenya da Habasha da Algeriya da Masar, amma har yanzu babu kasar da ta fi shigewa gaba wajen nema.

Tarayyar Afirka na da mambobi 55, kuma ana tunanin kungiyar ta zama wakiliyar nahiyar, amma Gowan ya ce kungiyar tana fama da cikas wajen aikin diflomaiyya.

Ya ce ana samun matsaloli da dama wajen daukar mataki a kungiyar, “misali kan matsalar da ta shafi Somalia,” in ji shi.

“Masana diflomasiyya dan Afirka da ke New York suna tunanin ya fi dacewa su rika daukar matakai daban da na takwarorinsu na Tarayyar Afirka saboda suna tunanin China da Amurka ba za su goyi bayan abin da kungiyar ke so ba.”

A yanzu da aka taru a birnin New York domin taron na Majalisar Dinkin Duniya, abin jira a gani shi ne shin Afirka za ta samu kujerar ta dindindin ko kuma kawai za a ci gaba da tafka muhawara ne.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutum Dubu 100 Tare Da Tarwatsa Mutane Miliyan 2 —Irabor
Manyan Labarai

Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor

October 12, 2025
Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
Labarai

Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

October 12, 2025
Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
Manyan Labarai

Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

October 12, 2025
Next Post
Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga 'Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

LABARAI MASU NASABA

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

October 12, 2025
‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutum Dubu 100 Tare Da Tarwatsa Mutane Miliyan 2 —Irabor

Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor

October 12, 2025
Yadda Ake Gurasa Ta Semovita

Yadda Ake Gurasa Ta Semovita

October 12, 2025
Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola

Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola

October 12, 2025
Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

October 12, 2025
Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya?

Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya?

October 12, 2025
Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

October 12, 2025
Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

October 11, 2025
Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

October 11, 2025
Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

October 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.