ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya?

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
8 months ago
Afirka

Amurka da China da Rasha ba su cika haduwa a teburi daya ba, duk da cewa akwai wasu abubuwan da dama da suke haduwa a kai.

Dukkansu sun amince nahiyar Afirka ta samu kujerar dindindin a kwamitin tsaro. Amma shin me ya sa har yanzu ba a tabbatar ba?

A kwamitin tsaro na MDD, akwai kasashe biyar masu kujerar dindindin wato China da Rasha da Faransa da Birtaniya da Amurka, wadanda ake kira da P5. Su kadai ne mambobin da suke da damar hawa kujerar na-ki.

ADVERTISEMENT

Sauran kasashen Majalisar Dinkin Duniya suna samun damar zama a kwamitin tsaron ne lokaci bayan lokaci, amma ba su da karfin ikon hawa kujerar na-ki.

‘Tabbatar da tsaron Afirka dole ne’

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya ce akwai bukatar gyara.

“Ba za a taba yi iya samar da tsaro a duniya ba, ba tare da tabbatar da tsaron Afirka ba,” in ji shi.

“Bai dace ba a ce kwamitin tsaro na duniya babu wakilcin nahiyar da ke da sama da mutum biliyan 1, wadda kuma mutanenta ke kara hayayyafa, kuma yanzu haka nahiyar ce ke da kashi 28 na kasashen Majalisar Dinkin Duniya.”

Kungiyar Tarayyar Afirka ta bukaci “akalla kujera biyu ta dindindin” da karfin ikon hawa kujerar na-ki, da kuma karin kujera biyar da ba na dindindin ba.

Amma duk da cewa yawancin kasashen majalisar sun amince akwai bukatar Afirka ta samu damar, masanin diflomasiyya a majalisar, Richard Gowan ya ce ya ce ba su shirya ba.

Gowan ya ce gwamnatin Amurka a karkashin Biden ta bayyana goyon bayanta kan yunkurin Afirka na samun kujera biyu, amma ba tare da karfin kujerar na-ki ba. Amma ya ce Trump ya nuna cewa ya fi son kwamitin a yadda yake, kuma ba ya so kasashe masu karfin hawa kujerar na-ki su yi yawa.

 

Wadanne kasashe daga Afirka?

Wata babbar matsalar da ke ci wa Afirka tuwo a kwarya ita ce shin wace kasa ce ta fi cancantar darewa kujerar guda daya ko biyu a kwamitin?

Kasashen da ake bayyanawa daga Afirka su ne Afirka ta Kudu da Nijeriya da Kenya da Habasha da Algeriya da Masar, amma har yanzu babu kasar da ta fi shigewa gaba wajen nema.

Tarayyar Afirka na da mambobi 55, kuma ana tunanin kungiyar ta zama wakiliyar nahiyar, amma Gowan ya ce kungiyar tana fama da cikas wajen aikin diflomaiyya.

Ya ce ana samun matsaloli da dama wajen daukar mataki a kungiyar, “misali kan matsalar da ta shafi Somalia,” in ji shi.

“Masana diflomasiyya dan Afirka da ke New York suna tunanin ya fi dacewa su rika daukar matakai daban da na takwarorinsu na Tarayyar Afirka saboda suna tunanin China da Amurka ba za su goyi bayan abin da kungiyar ke so ba.”

A yanzu da aka taru a birnin New York domin taron na Majalisar Dinkin Duniya, abin jira a gani shi ne shin Afirka za ta samu kujerar ta dindindin ko kuma kawai za a ci gaba da tafka muhawara ne.

Afirka
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga 'Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.