ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya?

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
9 months ago
Afirka

Amurka da China da Rasha ba su cika haduwa a teburi daya ba, duk da cewa akwai wasu abubuwan da dama da suke haduwa a kai.

Dukkansu sun amince nahiyar Afirka ta samu kujerar dindindin a kwamitin tsaro. Amma shin me ya sa har yanzu ba a tabbatar ba?

A kwamitin tsaro na MDD, akwai kasashe biyar masu kujerar dindindin wato China da Rasha da Faransa da Birtaniya da Amurka, wadanda ake kira da P5. Su kadai ne mambobin da suke da damar hawa kujerar na-ki.

ADVERTISEMENT

Sauran kasashen Majalisar Dinkin Duniya suna samun damar zama a kwamitin tsaron ne lokaci bayan lokaci, amma ba su da karfin ikon hawa kujerar na-ki.

‘Tabbatar da tsaron Afirka dole ne’

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya ce akwai bukatar gyara.

“Ba za a taba yi iya samar da tsaro a duniya ba, ba tare da tabbatar da tsaron Afirka ba,” in ji shi.

“Bai dace ba a ce kwamitin tsaro na duniya babu wakilcin nahiyar da ke da sama da mutum biliyan 1, wadda kuma mutanenta ke kara hayayyafa, kuma yanzu haka nahiyar ce ke da kashi 28 na kasashen Majalisar Dinkin Duniya.”

Kungiyar Tarayyar Afirka ta bukaci “akalla kujera biyu ta dindindin” da karfin ikon hawa kujerar na-ki, da kuma karin kujera biyar da ba na dindindin ba.

Amma duk da cewa yawancin kasashen majalisar sun amince akwai bukatar Afirka ta samu damar, masanin diflomasiyya a majalisar, Richard Gowan ya ce ya ce ba su shirya ba.

Gowan ya ce gwamnatin Amurka a karkashin Biden ta bayyana goyon bayanta kan yunkurin Afirka na samun kujera biyu, amma ba tare da karfin kujerar na-ki ba. Amma ya ce Trump ya nuna cewa ya fi son kwamitin a yadda yake, kuma ba ya so kasashe masu karfin hawa kujerar na-ki su yi yawa.

 

Wadanne kasashe daga Afirka?

Wata babbar matsalar da ke ci wa Afirka tuwo a kwarya ita ce shin wace kasa ce ta fi cancantar darewa kujerar guda daya ko biyu a kwamitin?

Kasashen da ake bayyanawa daga Afirka su ne Afirka ta Kudu da Nijeriya da Kenya da Habasha da Algeriya da Masar, amma har yanzu babu kasar da ta fi shigewa gaba wajen nema.

Tarayyar Afirka na da mambobi 55, kuma ana tunanin kungiyar ta zama wakiliyar nahiyar, amma Gowan ya ce kungiyar tana fama da cikas wajen aikin diflomaiyya.

Ya ce ana samun matsaloli da dama wajen daukar mataki a kungiyar, “misali kan matsalar da ta shafi Somalia,” in ji shi.

“Masana diflomasiyya dan Afirka da ke New York suna tunanin ya fi dacewa su rika daukar matakai daban da na takwarorinsu na Tarayyar Afirka saboda suna tunanin China da Amurka ba za su goyi bayan abin da kungiyar ke so ba.”

A yanzu da aka taru a birnin New York domin taron na Majalisar Dinkin Duniya, abin jira a gani shi ne shin Afirka za ta samu kujerar ta dindindin ko kuma kawai za a ci gaba da tafka muhawara ne.

Afirka
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga 'Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.