• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

by Abubakar Sulaiman
13 hours ago
Wike

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya zargi jam’iyyun adawa da haɗa kai da wasu ƙasashen waje wajen yaɗa labaran ƙarya cewa ana kisan Kiristoci a Nijeriya, yana mai cewa hakan “adawa ce da ta wuce gona da iri.” Wike ya bayyana haka ne a hirar da aka yi da shi a shirin Politics Today na Channels TV, inda ya mayar da martani kan kalaman Shugaban Amurka, Donald Trump, wanda ya zargi gwamnati da aikata kisan kiyashi kan Kiristoci.

Wike ya ce kalaman Trump sun dogara ne da siyasa da ƙarya, yana mai cewa gwamnati ba ta nuna bambancin addini. “Shugaban tsaro Kirista ne, IGP Kirista ne, SGF ma Kirista ne. To ta yaya gwamnati irin wannan za ta zartar da manufofin kisan Kiristoci?” in ji shi. Ya ƙara da cewa, matsalar tsaro da ake fuskanta ta shafi Kiristoci da Musulmai baki ɗaya, ba wani addini guda ba.

  • 2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi
  • PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

Tsohon gwamnan jihar Ribas ya kuma kare Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai cewa shugaban ƙasa ba mai tsattsauran ra’ayi ba ne. “Tinubu ya auri Kirista, kuma ya nuna ƙarfin hali wajen tabbatar da zaman lafiya tsakanin addinai. To me yasa za a ce yana da hannu wajen kisan Kiristoci? Wannan siyasa ce da ta wuce gona da iri,” in ji Wike.

Ya kuma tuna yadda irin wannan dabarar aka yi amfani da ita a 2015 domin ɓata tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, inda ƴan adawa suka yi amfani da labaran ƙarya wajen jawo rikicin addini. Wike ya yi gargaɗin cewa adawa na ƙoƙarin maimaita irin wannan dabarar ne yayin da ake tunkarar zaɓen 2027.

A cewar Wike, zargin da ake yi wa gwamnati a yanzu ba su da tushe, domin irin waɗannan kashe-kashe sun faru tun kafin Tinubu ya hau mulki. “A lokacin da aka sace ’yan matan Chibok ko lokacin kashe-kashen Benue, Tinubu ba shi ne shugaban ƙasa ba,” in ji shi. “Ba sai na zama Kirista ko Musulmi ba kafin in damu da mutuwar mutane, amma a yau, tabbas adawar ƴan siyasa ta wuce gona da iri.”

LABARAI MASU NASABA

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 
Manyan Labarai

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Manyan Labarai

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo
Manyan Labarai

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Next Post
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

LABARAI MASU NASABA

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.