ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Nemi Tinubu Ya Canza Salon Yaki

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
4 weeks ago
Majalisa

Majalisar Wakilai ta yi kira ga Shugaba Bola Tinubu da ya kirkiro sabon shiri domin kawo karshen kisan kai, satar mutane, da sauran ayyukan fashi da makami a Jihar Zamfara da kasar baki daya.

Wannan kira ya biyo bayan amincewa da tayin gaggawa na al’ummar kasa da dan majalisar da ke wakiltar Gusau/Tsafe Federal Constituency na Jihar Zamfara, Hon. Kabiru Amadu, ya gabatar a zaman majalisa ranar Talata.

  • Li Qian: Ya Kamata A Aiwatar Da Sakamakon Taron Kolin Tianjin Don Inganta Kungiyar SCO
  • Gwamnan Kano Ya Ɗauki Malaman Lissafi 400 Aiki

A yayin gabatar da tayin, Amadu ya bayyana cewa la’akari da matsalolin tsaro marasa iyaka a Jihar Zamfara da kasar baki daya, ya dace a ce “gwamnati ta yi isasshen aiki wajen kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Nijeriya domin su gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum.”

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa ’yan bindiga masu makamai masu karfi sun kai farmaki wasu sassan Jihar Zamfara inda suka kashe mutum sama da 10, sace mutane 130, sannan suka dora haraji mai yawa har Naira miliyan 100 ga wadannan al’ummomi masu rauni.

Amadu ya ce ’yan bindigan suna gudanar da laifukansu ne ta hanyar hawa babura, inda ba za ka rasa kasa da mutum biyu zuwa uku a kowane babur ba, suna zagayawa daga wani yanki zuwa wani tsawon makonni biyu zuwa uku, dauke da makamai ba tare da wani kalubale mai inganci daga hukumomin tsaro ba.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Ya nuna damuwarsa cewa, “Bukatar biyan Naira miliyan 100 a haraji ba dai-dai ba ne kuma ba mai yiwuwa ba ne ga jama’a da suka riga sun sha wahala saboda rasa rayuka da dukiyoyi, inda manyan ayyukan tattalin arzikinsu noma ce da kananan sana’o’i, wadanda duk sun sami matukar illa saboda tashin hankali da ke ci gaba da matsawa al’ummomin cikin talauci da damuwa mai zurfi.”

“Wannan rikici ya haifar da mawuyacin yanayin jin kai, inda mazauna ke rasa abubuwan bukatu na yau da kullum kamar abinci, kiwon lafiya da tsaro; tsoro yana mamaye su yayin da al’ummomi ke rayuwa karkashin barazanar sake kai farmaki da bukatar kudin fansa.

“Wannan kisan da aka ambata su kadai misalai ne daga cikin tarin kisan kai da satar mutane da suka faru a cikin wata guda kacal a mazabar da nake wakilta,” in ji shi yana nuna damuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Ribadu Ya Gana da Sakataren Yaƙin Amurka Kan Iƙirarin Kashe Kiristoci A Nijeriya

Ribadu Ya Gana da Sakataren Yaƙin Amurka Kan Iƙirarin Kashe Kiristoci A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.