• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Zama Babbar Lauya A Kotun Birtaniya —Munayah Hassan

by Bello Hamza
3 years ago
in Labarai
0
Yadda Na Zama Babbar Lauya A Kotun Birtaniya —Munayah Hassan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan Nijeriya musanmman ‘yan asalin yankin arewa na cigaba da yin fice a harkokin bunkasa rayuwar al’umma a sassan Duniya, ta baya-bayan nan ita ce, wata ‘yan asaloin Jihar Kano a Arewacin Nijeriya mai suna Munayah Yusuf Hassan wadda ta samu nasarar zama Mai Shari’a tare da kuma da gabatar da kara a Manyan Kotunan kasar Ingila da yankin Wales. 

Bayanin haka ya fito ne daga bakin wani shahafrraen Lauya mai zaman kansa kuma mai fafutukar kare hakkin al’umma a Nijeriya mai suna Bulama Bukarti.

  • ‘Muna Kira A Samar Da Jami’an Tsaro Na Yankin Arewacin Nijeriya’
  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu

Bayanin da LEADERSHIP Hausa ta samu ya nuna cewa, Munayah ta kammala digirinta na farko ne a fannin aikin lauya daga Jami’ar Bayero da ke Kano, ta kuma halarci Babban Makarantar Lauyoyi don kwarewa tare da zama cikakkiyar lauya a Nijeriya kafin daga nan ta koma kasa Birtaniya tare da mijinta wani kwarren mai ilimin zane-zane, don cigaba da rayuwa.

Daga nan ne ta shiga harkokin ta na shari’a a kotunan kasar Birtaniya inda har hukumar shari’ar kasar ta gano irin kwazon ta aka kuma nada a wannan matsayiin.

A mastayinta na mai shari’a a manyan kotunan Birtaniya da Wales, cikin aikinta shi ne shiryarwa tare da bayar da shawara ga masu shari’a da masu neman kariya a yayin da suke fuskantar shari’a a yankin na Birtaniya da Wales gaba daya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Suna kuma shiga tare da warware harkokin shari’a da suka hada da na kasuwanci, manyan laifukka, rikicerikice da suka shafi iyali da matsalolin yau da kullun a tsakanin al’umma.

A ranar Litinin ne aka kaddamar da Munayah a wata kayatacciyar biki da aka yi a Ingila inda ta ta yi rantsuwar yin aiki tukuru kamar yadda kundin tsarin mulkin Birtaniya ya samar ba tare da nuna banbancin addini ko kabilanci ba.

Munayah ta zama abin alfahari ga dukkan al’umma yankin arewacin Nijeriya musamman ganin ita ce mace ta farko da ta fara rike wannan matsayi na mai shari’a a manyan kotunan kasar Birtaniya, wannan na kuma zuwa ne a lokacin da ake ganin matan arewa a matsayin wadanda ke koma baya a fannin ilimi da harkokin cigaban al’umma.

Wannan nasara da Munayah ta samu kuma zai kara zaburar da mata da samari ‘yan arewa don su kara kaimin fuskantar karatukan su a fannoni da dama don suma su kai ga kololiyar nasara a bangaren da suka zaba wa kansu a duk inda suka samu kansu a fadin duniyar nan.

A tattanawar da ta yi da manema labarai bayan an rantsar da iya, Munayah Yusuf Hassan ta mika godiya ga Allah a bisa wannan nasarar da ta samu ta kuma gode wa mijinta da sauran ‘yan uwa a kan irin goyon bayan da suka bata a dukkan lokutta har ta kai ga samun wannan nasarar.

Muna addu’ar Allah ya sa wannan ya zama sanadiyyar daukaka ga Munayah, ‘yanuwa da abokan arzikinta da al’ummar yankin arewa dama Nijeriya gaba daya, da fatan kuma zai zama wani matakala na daukaka da abin koyi ga matasanmu na yankin Arewa don su kara kaimi a harkokin su na rayuwa daban-daban.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bulama BukartiIngilaLauyaMunayahWales
ShareTweetSendShare
Previous Post

Iyaye 34 Suka Yi Wa ‘Ya’yansu 48 Fyade Cikin Shekara 2

Next Post

Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

34 minutes ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

2 hours ago
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 
Manyan Labarai

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

3 hours ago
Labarai

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

6 hours ago
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya
Labarai

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

7 hours ago
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru
Manyan Labarai

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

9 hours ago
Next Post
Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa

Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.