ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Zama Babbar Lauya A Kotun Birtaniya —Munayah Hassan

by Bello Hamza
4 years ago
Babbar Lauya

‘Yan Nijeriya musanmman ‘yan asalin yankin arewa na cigaba da yin fice a harkokin bunkasa rayuwar al’umma a sassan Duniya, ta baya-bayan nan ita ce, wata ‘yan asaloin Jihar Kano a Arewacin Nijeriya mai suna Munayah Yusuf Hassan wadda ta samu nasarar zama Mai Shari’a tare da kuma da gabatar da kara a Manyan Kotunan kasar Ingila da yankin Wales. 

Bayanin haka ya fito ne daga bakin wani shahafrraen Lauya mai zaman kansa kuma mai fafutukar kare hakkin al’umma a Nijeriya mai suna Bulama Bukarti.

  • ‘Muna Kira A Samar Da Jami’an Tsaro Na Yankin Arewacin Nijeriya’
  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu

Bayanin da LEADERSHIP Hausa ta samu ya nuna cewa, Munayah ta kammala digirinta na farko ne a fannin aikin lauya daga Jami’ar Bayero da ke Kano, ta kuma halarci Babban Makarantar Lauyoyi don kwarewa tare da zama cikakkiyar lauya a Nijeriya kafin daga nan ta koma kasa Birtaniya tare da mijinta wani kwarren mai ilimin zane-zane, don cigaba da rayuwa.

ADVERTISEMENT

Daga nan ne ta shiga harkokin ta na shari’a a kotunan kasar Birtaniya inda har hukumar shari’ar kasar ta gano irin kwazon ta aka kuma nada a wannan matsayiin.

A mastayinta na mai shari’a a manyan kotunan Birtaniya da Wales, cikin aikinta shi ne shiryarwa tare da bayar da shawara ga masu shari’a da masu neman kariya a yayin da suke fuskantar shari’a a yankin na Birtaniya da Wales gaba daya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Suna kuma shiga tare da warware harkokin shari’a da suka hada da na kasuwanci, manyan laifukka, rikicerikice da suka shafi iyali da matsalolin yau da kullun a tsakanin al’umma.

A ranar Litinin ne aka kaddamar da Munayah a wata kayatacciyar biki da aka yi a Ingila inda ta ta yi rantsuwar yin aiki tukuru kamar yadda kundin tsarin mulkin Birtaniya ya samar ba tare da nuna banbancin addini ko kabilanci ba.

Munayah ta zama abin alfahari ga dukkan al’umma yankin arewacin Nijeriya musamman ganin ita ce mace ta farko da ta fara rike wannan matsayi na mai shari’a a manyan kotunan kasar Birtaniya, wannan na kuma zuwa ne a lokacin da ake ganin matan arewa a matsayin wadanda ke koma baya a fannin ilimi da harkokin cigaban al’umma.

Wannan nasara da Munayah ta samu kuma zai kara zaburar da mata da samari ‘yan arewa don su kara kaimin fuskantar karatukan su a fannoni da dama don suma su kai ga kololiyar nasara a bangaren da suka zaba wa kansu a duk inda suka samu kansu a fadin duniyar nan.

A tattanawar da ta yi da manema labarai bayan an rantsar da iya, Munayah Yusuf Hassan ta mika godiya ga Allah a bisa wannan nasarar da ta samu ta kuma gode wa mijinta da sauran ‘yan uwa a kan irin goyon bayan da suka bata a dukkan lokutta har ta kai ga samun wannan nasarar.

Muna addu’ar Allah ya sa wannan ya zama sanadiyyar daukaka ga Munayah, ‘yanuwa da abokan arzikinta da al’ummar yankin arewa dama Nijeriya gaba daya, da fatan kuma zai zama wani matakala na daukaka da abin koyi ga matasanmu na yankin Arewa don su kara kaimi a harkokin su na rayuwa daban-daban.

Babbar Lauya
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa

Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.