ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Zama Babbar Lauya A Kotun Birtaniya —Munayah Hassan

by Bello Hamza
4 years ago
Babbar Lauya

‘Yan Nijeriya musanmman ‘yan asalin yankin arewa na cigaba da yin fice a harkokin bunkasa rayuwar al’umma a sassan Duniya, ta baya-bayan nan ita ce, wata ‘yan asaloin Jihar Kano a Arewacin Nijeriya mai suna Munayah Yusuf Hassan wadda ta samu nasarar zama Mai Shari’a tare da kuma da gabatar da kara a Manyan Kotunan kasar Ingila da yankin Wales. 

Bayanin haka ya fito ne daga bakin wani shahafrraen Lauya mai zaman kansa kuma mai fafutukar kare hakkin al’umma a Nijeriya mai suna Bulama Bukarti.

  • ‘Muna Kira A Samar Da Jami’an Tsaro Na Yankin Arewacin Nijeriya’
  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu

Bayanin da LEADERSHIP Hausa ta samu ya nuna cewa, Munayah ta kammala digirinta na farko ne a fannin aikin lauya daga Jami’ar Bayero da ke Kano, ta kuma halarci Babban Makarantar Lauyoyi don kwarewa tare da zama cikakkiyar lauya a Nijeriya kafin daga nan ta koma kasa Birtaniya tare da mijinta wani kwarren mai ilimin zane-zane, don cigaba da rayuwa.

ADVERTISEMENT

Daga nan ne ta shiga harkokin ta na shari’a a kotunan kasar Birtaniya inda har hukumar shari’ar kasar ta gano irin kwazon ta aka kuma nada a wannan matsayiin.

A mastayinta na mai shari’a a manyan kotunan Birtaniya da Wales, cikin aikinta shi ne shiryarwa tare da bayar da shawara ga masu shari’a da masu neman kariya a yayin da suke fuskantar shari’a a yankin na Birtaniya da Wales gaba daya.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Suna kuma shiga tare da warware harkokin shari’a da suka hada da na kasuwanci, manyan laifukka, rikicerikice da suka shafi iyali da matsalolin yau da kullun a tsakanin al’umma.

A ranar Litinin ne aka kaddamar da Munayah a wata kayatacciyar biki da aka yi a Ingila inda ta ta yi rantsuwar yin aiki tukuru kamar yadda kundin tsarin mulkin Birtaniya ya samar ba tare da nuna banbancin addini ko kabilanci ba.

Munayah ta zama abin alfahari ga dukkan al’umma yankin arewacin Nijeriya musamman ganin ita ce mace ta farko da ta fara rike wannan matsayi na mai shari’a a manyan kotunan kasar Birtaniya, wannan na kuma zuwa ne a lokacin da ake ganin matan arewa a matsayin wadanda ke koma baya a fannin ilimi da harkokin cigaban al’umma.

Wannan nasara da Munayah ta samu kuma zai kara zaburar da mata da samari ‘yan arewa don su kara kaimin fuskantar karatukan su a fannoni da dama don suma su kai ga kololiyar nasara a bangaren da suka zaba wa kansu a duk inda suka samu kansu a fadin duniyar nan.

A tattanawar da ta yi da manema labarai bayan an rantsar da iya, Munayah Yusuf Hassan ta mika godiya ga Allah a bisa wannan nasarar da ta samu ta kuma gode wa mijinta da sauran ‘yan uwa a kan irin goyon bayan da suka bata a dukkan lokutta har ta kai ga samun wannan nasarar.

Muna addu’ar Allah ya sa wannan ya zama sanadiyyar daukaka ga Munayah, ‘yanuwa da abokan arzikinta da al’ummar yankin arewa dama Nijeriya gaba daya, da fatan kuma zai zama wani matakala na daukaka da abin koyi ga matasanmu na yankin Arewa don su kara kaimi a harkokin su na rayuwa daban-daban.

Babbar Lauya
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa

Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.