• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Yobe Ta Tallafa Wa Magidanta 457 A Karamar Hukumar Jakusko

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Yobe Ta Tallafa Wa Magidanta 457 A Karamar Hukumar Jakusko
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon mawuyacin halin da ambaliyar ruwa ta jefa daruruwan al’umma a sassa daban-daban a jihar, gwamnatin Jihar Yobe ta hannun Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa (SEMA) tare da hadin gwiwar NEMA, sun raba kayan tallafi ga magidanta 457 wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a kauyuka 17 da ke karamar hukumar Jakusko a Jihar Yobe.

Hukumar SEMA ta gudanar da raba tallafa wa wadanda ibtila’in ambaliyar ruwa ya shafa da kayan abinci, kwanon rufi, buhunan siminti, katifu da makamantan su a kauyukan Girgir, Katamma, Amshi, Guyik, Muguram, Jaba, Jakusko, Dumbari, Gwayo, Dukorel, Lafiya, Bayam, Buduwa, Saminaka, Garin Saje, Dachiya da Zabudum, duk a karamar hukumar Jakusko.

  • Xi Ya Halarcin Majalisar Shugabannin Kasashen SCO Karo Na 22 Tare Da Gabatar Da Muhimmin Jawabi
  • Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zarce Yadda Ake Tsammani

A zantawarsa da wakilinmu a jihar, Shugaban Hukumar SEMA, Dr Muhammed Goje ya bayyana cewa sun fara samun koke-koken al’ummar wadannan garuruwa dangane da ambaliyar ruwa tun a watan Yuli zuwa Agusta, wanda ta hadin gwiwa da karamar hukumar Jakusko sun gudanar da tantancewa tare da bayyana wadanda abin ya shafa.

Ya ce, “A yau 16 ga watan Satumban 2022, mun raba kayan tallafi ta hadin gwiwar NEMA wanda gwamnatin tarayya ta bayar da nata gudumawa ga wadanda ibtila’in ambaliyar ruwa ya shafa, wanda adadin su ya haura magidanta 400.”

Bugu da kari kuma, a daidai wannan lokaci inda muke raba kayan tallafin, sai kuma ga karin wata ambaliyar ruwa ta abka a wadannan garuruwa, wanda suma yanzu haka suna cikin mawuyacin halin bukatar tallafi.

Labarai Masu Nasaba

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

Saboda haka, tawagar ma’aikatan SEMA za su ci gaba da aiki da karamar hukumar Jakusko domin shiga kowane sako wajen tantance kima da adadin mutanen da wannan ambaliyar ruwan ta shafa, domin ci gaba da tallafa musu kamar yadda Gwamna Mai Mala Buni ya umurce mu.

Ya ce, “Haka kuma, bisa ga halin da ambaliyar ruwan ta jefa jama’a ciki, muna raba wadannan kayan ginin, katifu tare da kayan abinci kai tsaye zuwa ga magidantan da abin ya shafa. Sannan kuma tawagar SEMA da ta karamar hukumar Jakusko za su ci gaba da daukar matakan gaggawa wajen kai dauki ga wadanda abin ya shafa cikin hanzari, kuma a tantance su tare da raba tallafin kai tsaye ga jama’a.”

Karamar hukumar Jakusko da sauran masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun yaba wa kokarin gwamnatin jihar Yobe bisa daukin gaggawa da ta kawo wa jama’a a kan lokaci tare da yin kira ga wadanda abin ya shafa da su yi amfani da tallafin cikin adalci domin lamarin ba biyansu asarar da suka yi ba ne, face tallafi ne.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwaNEMASEMATallafiYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Halarcin Majalisar Shugabannin Kasashen SCO Karo Na 22 Tare Da Gabatar Da Muhimmin Jawabi

Next Post

Gwamnonin Arewa Maso Gabas Za Su Samar Da Kamfanin Zirga-zirgan Jirgin Sama

Related

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

3 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

4 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

5 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

6 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

7 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

11 hours ago
Next Post
Gwamnonin Arewa Maso Gabas Za Su Samar Da Kamfanin Zirga-zirgan Jirgin Sama

Gwamnonin Arewa Maso Gabas Za Su Samar Da Kamfanin Zirga-zirgan Jirgin Sama

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.