• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Yobe Ta Tallafa Wa Magidanta 457 A Karamar Hukumar Jakusko

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Yobe Ta Tallafa Wa Magidanta 457 A Karamar Hukumar Jakusko
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon mawuyacin halin da ambaliyar ruwa ta jefa daruruwan al’umma a sassa daban-daban a jihar, gwamnatin Jihar Yobe ta hannun Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa (SEMA) tare da hadin gwiwar NEMA, sun raba kayan tallafi ga magidanta 457 wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a kauyuka 17 da ke karamar hukumar Jakusko a Jihar Yobe.

Hukumar SEMA ta gudanar da raba tallafa wa wadanda ibtila’in ambaliyar ruwa ya shafa da kayan abinci, kwanon rufi, buhunan siminti, katifu da makamantan su a kauyukan Girgir, Katamma, Amshi, Guyik, Muguram, Jaba, Jakusko, Dumbari, Gwayo, Dukorel, Lafiya, Bayam, Buduwa, Saminaka, Garin Saje, Dachiya da Zabudum, duk a karamar hukumar Jakusko.

  • Xi Ya Halarcin Majalisar Shugabannin Kasashen SCO Karo Na 22 Tare Da Gabatar Da Muhimmin Jawabi
  • Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zarce Yadda Ake Tsammani

A zantawarsa da wakilinmu a jihar, Shugaban Hukumar SEMA, Dr Muhammed Goje ya bayyana cewa sun fara samun koke-koken al’ummar wadannan garuruwa dangane da ambaliyar ruwa tun a watan Yuli zuwa Agusta, wanda ta hadin gwiwa da karamar hukumar Jakusko sun gudanar da tantancewa tare da bayyana wadanda abin ya shafa.

Ya ce, “A yau 16 ga watan Satumban 2022, mun raba kayan tallafi ta hadin gwiwar NEMA wanda gwamnatin tarayya ta bayar da nata gudumawa ga wadanda ibtila’in ambaliyar ruwa ya shafa, wanda adadin su ya haura magidanta 400.”

Bugu da kari kuma, a daidai wannan lokaci inda muke raba kayan tallafin, sai kuma ga karin wata ambaliyar ruwa ta abka a wadannan garuruwa, wanda suma yanzu haka suna cikin mawuyacin halin bukatar tallafi.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

GORON JUMA’A 09/05/2025

Saboda haka, tawagar ma’aikatan SEMA za su ci gaba da aiki da karamar hukumar Jakusko domin shiga kowane sako wajen tantance kima da adadin mutanen da wannan ambaliyar ruwan ta shafa, domin ci gaba da tallafa musu kamar yadda Gwamna Mai Mala Buni ya umurce mu.

Ya ce, “Haka kuma, bisa ga halin da ambaliyar ruwan ta jefa jama’a ciki, muna raba wadannan kayan ginin, katifu tare da kayan abinci kai tsaye zuwa ga magidantan da abin ya shafa. Sannan kuma tawagar SEMA da ta karamar hukumar Jakusko za su ci gaba da daukar matakan gaggawa wajen kai dauki ga wadanda abin ya shafa cikin hanzari, kuma a tantance su tare da raba tallafin kai tsaye ga jama’a.”

Karamar hukumar Jakusko da sauran masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun yaba wa kokarin gwamnatin jihar Yobe bisa daukin gaggawa da ta kawo wa jama’a a kan lokaci tare da yin kira ga wadanda abin ya shafa da su yi amfani da tallafin cikin adalci domin lamarin ba biyansu asarar da suka yi ba ne, face tallafi ne.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwaNEMASEMATallafiYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Halarcin Majalisar Shugabannin Kasashen SCO Karo Na 22 Tare Da Gabatar Da Muhimmin Jawabi

Next Post

Gwamnonin Arewa Maso Gabas Za Su Samar Da Kamfanin Zirga-zirgan Jirgin Sama

Related

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

35 minutes ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

2 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

3 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

4 hours ago
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote
Labarai

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

5 hours ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

6 hours ago
Next Post
Gwamnonin Arewa Maso Gabas Za Su Samar Da Kamfanin Zirga-zirgan Jirgin Sama

Gwamnonin Arewa Maso Gabas Za Su Samar Da Kamfanin Zirga-zirgan Jirgin Sama

LABARAI MASU NASABA

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.