• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Yobe Ta Tallafa Wa Magidanta 457 A Karamar Hukumar Jakusko

by Muhammad Maitela
3 years ago
Ambaliyar Ruwa

Sakamakon mawuyacin halin da ambaliyar ruwa ta jefa daruruwan al’umma a sassa daban-daban a jihar, gwamnatin Jihar Yobe ta hannun Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa (SEMA) tare da hadin gwiwar NEMA, sun raba kayan tallafi ga magidanta 457 wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a kauyuka 17 da ke karamar hukumar Jakusko a Jihar Yobe.

Hukumar SEMA ta gudanar da raba tallafa wa wadanda ibtila’in ambaliyar ruwa ya shafa da kayan abinci, kwanon rufi, buhunan siminti, katifu da makamantan su a kauyukan Girgir, Katamma, Amshi, Guyik, Muguram, Jaba, Jakusko, Dumbari, Gwayo, Dukorel, Lafiya, Bayam, Buduwa, Saminaka, Garin Saje, Dachiya da Zabudum, duk a karamar hukumar Jakusko.

  • Xi Ya Halarcin Majalisar Shugabannin Kasashen SCO Karo Na 22 Tare Da Gabatar Da Muhimmin Jawabi
  • Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zarce Yadda Ake Tsammani

A zantawarsa da wakilinmu a jihar, Shugaban Hukumar SEMA, Dr Muhammed Goje ya bayyana cewa sun fara samun koke-koken al’ummar wadannan garuruwa dangane da ambaliyar ruwa tun a watan Yuli zuwa Agusta, wanda ta hadin gwiwa da karamar hukumar Jakusko sun gudanar da tantancewa tare da bayyana wadanda abin ya shafa.

Ya ce, “A yau 16 ga watan Satumban 2022, mun raba kayan tallafi ta hadin gwiwar NEMA wanda gwamnatin tarayya ta bayar da nata gudumawa ga wadanda ibtila’in ambaliyar ruwa ya shafa, wanda adadin su ya haura magidanta 400.”

Bugu da kari kuma, a daidai wannan lokaci inda muke raba kayan tallafin, sai kuma ga karin wata ambaliyar ruwa ta abka a wadannan garuruwa, wanda suma yanzu haka suna cikin mawuyacin halin bukatar tallafi.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Saboda haka, tawagar ma’aikatan SEMA za su ci gaba da aiki da karamar hukumar Jakusko domin shiga kowane sako wajen tantance kima da adadin mutanen da wannan ambaliyar ruwan ta shafa, domin ci gaba da tallafa musu kamar yadda Gwamna Mai Mala Buni ya umurce mu.

Ya ce, “Haka kuma, bisa ga halin da ambaliyar ruwan ta jefa jama’a ciki, muna raba wadannan kayan ginin, katifu tare da kayan abinci kai tsaye zuwa ga magidantan da abin ya shafa. Sannan kuma tawagar SEMA da ta karamar hukumar Jakusko za su ci gaba da daukar matakan gaggawa wajen kai dauki ga wadanda abin ya shafa cikin hanzari, kuma a tantance su tare da raba tallafin kai tsaye ga jama’a.”

Karamar hukumar Jakusko da sauran masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun yaba wa kokarin gwamnatin jihar Yobe bisa daukin gaggawa da ta kawo wa jama’a a kan lokaci tare da yin kira ga wadanda abin ya shafa da su yi amfani da tallafin cikin adalci domin lamarin ba biyansu asarar da suka yi ba ne, face tallafi ne.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Gwamnonin Arewa Maso Gabas Za Su Samar Da Kamfanin Zirga-zirgan Jirgin Sama

Gwamnonin Arewa Maso Gabas Za Su Samar Da Kamfanin Zirga-zirgan Jirgin Sama

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.