• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Xi Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Da Dama

by CMG Hausa
3 years ago
Shugaba Xi

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bayyana aniyarsa ta aiki tare da kasar Rasha, don karfafa taimakon juna kan batutuwan dake shafar babbar moriyar sassan biyu.

Shugaba Xi ya bayyana hakan ne, yayin da yake zantawa da takwaransa na Rasha Vladimir Putin, jiya Alhamis a babban ginin Forumlar Majmuasi na birnin Samarkand dake kasar Uzbekistan.

  • Shugaban Kasar Ukraine, Zelensky Ya Yi Hadarin Mota

Shugabannin biyu sun gane domin yin musaya, game da batutuwan da suka shafi kasashensu a mataki na kasa da kasa da na shiyyoyi. Xi ya ce a wannan gaba da duniya ke fuskantar sauye-sauye, Sin za ta yi aiki tukuru tare da Rasha, don sauke nauyin dake wuyansu, a matsayin su na manyan kasashe, za su kuma yi rawar gani wajen ingiza samar da daidaito, a duniya dake fama da sauyi da rashin daidaito.

A nasa bangare kuwa, shugaba Putin ya yiwa JKS fatan samun nasara a babban taron ta karo na 20 da za a shirya a wata mai zuwa. Yana mai imanin cewa, karkashin jagorancin shugaba Xi, Sin za ta ci gaba da cimma manyan nasarori a fannin tattalin arziki da zamantakewar al’umma.

Shugaban na Rsaha ya kara da cewa, duniya na fuskantar manyan sauye sauye, amma duk da haka, kawance da aminci dake tsakanin Sin da Rasha bai sauya ba.

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Kaza lika sassan biyu na ci gaba da raya cikakken hadin gwiwa dake tsakaninsu yadda ya kamata. Ya ce Rasha da Sin, sun amince da bin tsarin gudanar da duniya mai ma’ana bisa adalci, suna kuma kafa misali na kyakkyawan hadin gwiwar kasa da kasa ga duniya.

Baya ga shugaba Putin, shugaba Xi ya kuma gana da shugaban kasar Azerbaijani Ilham Aliyev, da na Belarus Alexander Lukashenko, da na Mongolia Ukhnaa Khurelsukh, da na Iran Seyed Ebrahim Raisi, da na Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, da kuma firaministan kasar Pakistan Muhammad Shahbaz Sharif.

Bugu da kari, ya jagoranci taro karo na 6 na kasashen Sin da Rasha da Mongolia a ranar 15 zuwa 16 ga wata. (Mai Fassarawa: Saminu Alhassan)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
Daga Birnin Sin

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Daga Birnin Sin

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 2, 2025
Next Post
Sin Ta Tallafa Wa Falasdin Da Kudi Dala Miliyan 1 Don Inganta Ilimin Yara

Sin Ta Tallafa Wa Falasdin Da Kudi Dala Miliyan 1 Don Inganta Ilimin Yara

LABARAI MASU NASABA

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

November 3, 2025
Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

November 3, 2025
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.