• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Farmaki Hadimin Gwamnan Bauchi, Sun Jikkata Mutum 1

by Khalid Idris Doya
3 years ago
'Yansanda

Wasu ‘yan bindigan da ba a gano ko su waye ba zuwa yanzu sun kai hari gidan babban mai taimaka wa gwamnan Jihar Bauchi kan harkokin kula da Kiristoci, Fasto Zakka Luka Magaji a gidansa da ke kauyen Birshi da ke cikin garin Bauchi.

‘Yan bindigan da yawansu ya kai bakwai sun mamaye gidan Luka ne da kokarin yin garkuwa da shi ko barazana ga rayuwarsa. Amma cikin ikon Allah basu samu nasarar hakan ba 

  • Kamfanonin Kasar Sin Sun Shirya Taron Horar Da Matasan Afrika
  • Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zarce Yadda Ake Tsammani

A lokacin harin, wani matashi mai shekara 32 da ya kasance mambar cocin Christian Life da ke zaune tare da Fasto Zakka din an jikkata shi.

A lokacin da kwamishinan kula da harkokin addinai na jihar Bauchi, Hon Umar Babayo Kesa ya jagoranci tawagar ma’aikatarsa don kai ziyarar jaje ga Faston, Zakka ya shaida cewa ba su san dalilin wadanda suka kawo masa harin ba, “Amma cikin ikon Allah, Allah ya karemu. Kuma wadda ya jikkatan zuwa yanzu yana samun sauki.”

A nasa fannin, Umar Babayo Kesa, ya shaida cewar sun zo ne domin jajanta wa Faston bisa wannan harin da aka kai masa. 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

Ya yi addu’ar Allah ya cigaba kare shi da iyalansa daga hannun miyagun. 

Faston ya gode musu bisa wannan ziyarar ya nuna hakan a matsayin matakin da zai Kara kyautata zaman lafiya a tsakanin al’ummar jihar.

Ita ma rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, ta tabbatar da faruwar lamarin ta bakin kakakinta, Ahmed Wakil, inda ya ce tunin aka fara kokarin cafko maharan.

Ya ce, rundunar ta samu kiran waya kan lamarin wajajen karfe 0013hrs inda suka dauki matakin tura jami’ai da kai daukin gaggawa.

Ya ce lokacin da jami’an ‘yansandan suka isa wajen, sun samu kwanson harsasai uku samfurin 7.6mm.

Wakil ya kara da cewa sun dauki wadda aka jikkata zuwa asibitin ATBUTH domin kulawar Likitoci  

Ya cigaba da cewa suna kokarin daukan matakan da suka dace domin cafko wadanda suka kai wannan harin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum
Manyan Labarai

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
Labarai

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano
Manyan Labarai

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Next Post
FBI Na Neman Wani Dan Nijeriya Da Ya Damfari Amurka Dala Miliyan 30

FBI Na Neman Wani Dan Nijeriya Da Ya Damfari Amurka Dala Miliyan 30

LABARAI MASU NASABA

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

October 26, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

October 26, 2025
Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

October 26, 2025
Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.