• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Tana Kawo Tabbaci Ga Duniya Yayin Da Take Cikin Yanayi Na Tangal-Tangal

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Tana Kawo Tabbaci Ga Duniya Yayin Da Take Cikin Yanayi Na Tangal-Tangal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka kasashen duniya suna cikin yanayi mai sarkakiya, kuma ba a kai ga shawo kan annobar cutar COVID-19 ba tukuna, kana tattalin arzikin duniya yana kara fuskantar koma baya, baya ga matsalar karancin makamashi da hatsi sakamakon tsananta rikicin Ukraine.

A hannu guda kuma tunanin yakin cacar baki, da siyasar nuna fin karfi, da ra’ayin bangaranci da kare moriyar kashin kai, sun sake bulla a fadin duniya.

  • Adadin Kudin Shigar Kayayyakin Manhajar Masana’antun Sin A Watanni 7 Na Farkon Bana Ya Karu Da Kaso 8.7 Bisa Dari

A game da wannan batu, a jawabin da ya gabatar yayin taron muhawara na babban taron MDD karo na 77, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya sake yin bayani kan shawarwarin tabbatar da tsaron duniya da raya duniya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, inda ya zayyana manufofi shida, wadanda suke tabbatar da wanzar da zaman lafiya a maimakon rikici, da raya kasa a maimakon talauci, da bude kofa ga ketare a maimakon rufe kofa, da gudanar da hadin gwiwa a maimakon nuna kiyayya, da hada kai a maimakon kawo baraka, da tabbatar da adalci a maimakon nuna fin karfi, manufofin dake nuna matsayin kasar Sin game da muhimman batutuwan da suka shafi harkokin kasa da kasa.

Shugaban babban taron MDD karo na 77 Korosi Csaba, ya yi nuni da cewa, kasar Sin tana taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa, kuma muhimman shawarwarin da shugaba Xi Jinping ya gabatar, su ma sun samar da dabarun daidaita kalubalolin da kasashen duniya ke fuskanta a halin da ake ciki yanzu.

Shi ma babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya yaba wa muhimmiyar rawar da kasar Sin da dade tana takawa, wajen goyon bayan manufar tafiyar da harkokin kasa da kasa tsakanin bangarori daban daban, da ingiza hadin gwiwar dake tsakanin kasa da kasa, da samun dauwamammen ci gaba da sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

Yana mai bayyana cewa, MDD tana goyon bayan shawarar raya kasashen duniya baki daya da shugaba Xi ya gabatar, yana mai cike da imani cewa, shawarar za ta taimakawa yunkurin samun dauwamammen ci gaban duniya nan da shekarar 2030.

Duk da cewa, kalulabe da kasashen duniya suke fuskanta, kasar Sin tana taka muhimmiyar rawar da ta dace don ganin kwalliya ta biya kudin sabulu. (Mai fassarawa: Jamila daga CMG Hausa)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kusan Kasashe 70 Sun Nuna Rashin Amincewarsu Da Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar Sin

Next Post

Tsohon Kaftin Din Super Eagles, Mikel Obi Ya Yi Ritaya Daga Buga Kwallon Kafa

Related

Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho
Daga Birnin Sin

Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

57 minutes ago
Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu
Daga Birnin Sin

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

2 hours ago
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

13 hours ago
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa
Daga Birnin Sin

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

21 hours ago
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba
Daga Birnin Sin

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

22 hours ago
Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

23 hours ago
Next Post
Tsohon Kaftin Din Super Eagles, Mikel Obi Ya Yi Ritaya Daga Buga Kwallon Kafa

Tsohon Kaftin Din Super Eagles, Mikel Obi Ya Yi Ritaya Daga Buga Kwallon Kafa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

July 9, 2025
Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal

Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal

July 9, 2025
Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

July 9, 2025
Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

July 9, 2025
Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

July 9, 2025
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya BuÆ™aci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.