• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Zaɓe: Mun Ƙwace Katin Zaɓe Da Shaidar Ɗan Ƙasa 526 Daga ‘Yan Ƙasar Waje – Shugaban NIS

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
Shirin Zaɓe: Mun Ƙwace Katin Zaɓe Da Shaidar Ɗan Ƙasa 526 Daga ‘Yan Ƙasar Waje – Shugaban NIS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), CGI Isah Jere Idris ya bayyana cewa hukumarsa ta ƙwace katin zaɓe da aƙalla katin shaidar zama ɗan ƙasa 526 daga hannun baƙi ‘yan ƙasar waje a faɗin Nijeriya.

Ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabin buɗe wani taron da ya kira ɗaukacin manyan kwanturololin hukumar da ke sassa daban-daban na ƙasa domin shirin tunkarar ayyukan da hukumar za ta yi yayin gudanar da harkokin zaɓen 2023.

“Bisa tsarin jadawalin zaɓe na ƙasa, a yau (Laraba) jam’iyyu ke fara yaƙin neman zaɓe. A ƙoƙarin da muke yi na fara kimtsa jami’anmu manya da ƙanana domin tunkarar shirye-shiryen zaɓen da wuri, na gayyato Kwanturololin Manyan Ofisoshinmu na Jihohi domin mu ƙarfafa sintiri a iyakokin ƙasa a wannan lokacin. Ana sa ran su yi haɗin gwiwa da sauran hukumomi wajen hana kwararowar baƙin-haure da bazuwar ƙananan makamai wanda ka iya kawo cikas ga gudanar da zaɓe cikin kwanciyar hankali da lumana.

“Bugu da ƙari za mu ruɓanya ƙoƙarinmu wajen gudanar da sintiri da sanya idanu sosai a duk faɗin ƙasar nan. Za mu yi haka ne domin tabbatar da cewa babu wani ɗan ƙasar waje da aka bari ya yi ya kaɗa ƙuri’a a zaɓen ko kuma ya haddasa fitina a wannan lokacin mai muhimmanci.” In ji shi.

  • Kotu Ta Tabbatar Da Machina A Matsayin Dan Takarar Sanatan APC A Mazabar Yobe Ta Arewa

Isah Jere ya ce hukumar ta duƙufa ka’in da na’in wajen tabbatar da cewa babu wani baƙo da aka bari ya yi katsalandan a zaɓen na 2023.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

“Tuni muka ƙwace katinan zaɓe da na shaidar zama ɗan ƙasa na NIMC. Daga bayanan da muke da su a yau, akwai katin ɗan ƙasa 526 da muka ƙwace daga ‘yan ƙasashen waje waɗanda suka mallaka ta haramtattun hanyoyi. Nan da ‘yan kwanaki masu zuwa, muna sa ran ƙwace ƙarin wasu a sassa daban-daban na ofisoshinmu da ke ƙasar nan.”

NIS
Dandazon Kwanturololin Jihohi na NIS da suka halarci taron

Wakazalika, shugaban hukumar ta NIS ya gargaɗi dukkan manyan jami’an da ke shugabantar sassan hukumar kar su kuskura su bari a haɗa baki da su don mara wa wata jam’iyya baya, yana mai cewa duk wanda aka kama da laifin hakan zai ɗanɗana kuɗarsa.

“Akwai buƙatar kwanturololi na jihohi su ƙara zage damtse a wannan lokacin wajen gudanar da ayyukansu, domin duk wani abu da aka aikata da ya saɓa wa ƙa’idar aiki akwai hukunci a kai daidai da yadda dokar aikin gwamnati ta tanada.”

Har ila yau, CGI Jere ya nemi haɗin kan ‘yan jarida wajen samun nasarar ayyukan da suke gudanarwa, domin a cewarsa, “`yan jarida kuna daga cikin masu ruwa da tsaki. Labarun da kuke tattarowa yayin gudanar da ayyukanku za su iya taimakawa gaya wajen magance matsalolin tsaron ƙasa.

“Mu a NIS, mun yi ammanar cewa haɗin gwiwa da dukkan masu ruwa da tsaki yana da matuƙar muhimmanci wajen samun nasarar ayyukanmu. A kan haka, muna maraba da duk wani abu na kishin ƙasa da za a haɗa hannu da mu a kai domin tabbatar da ci gaban ƙasar da muke fatan gani a Nijeriya.

“Ina tabbatar muku da cewa a kullum ƙofarmu a buɗe take wajen karɓar bayanai da za su taimake mu gudanar da aiki tuƙuru ga ƙasa, sannan ina kira gare ku a koyaushe ku riƙa gudanar da sahihin bincike a kan duk wani labari da kuka ji a game da mu. Wannan roƙo ne na neman adalci da muke muku saboda bai saɓa wa ƙa’idar aikin jarida ba wadda ta jaddada buƙatar yi wa kowane ɓangare adalci wajen tuntuɓa don a ji ta bakinsa. A madadin mahukuntan NIS da ɗaukacin jami’anta, muna godiya da kuka amsa gayyatarmu.” Ya bayyana.

  • https://leadership.ng/nis-unodc-unveil-report-on-migrants-smuggling/

Da suke tofa albarkacin bakinsu daban-daban, Kwanturolan NIS na Jihar Bayelsa, CI Sunday James da takwaransa na iyakar ƙasa ta Jibiya, CI Kelechi Ekeoba da kuma ta Filin Jiragen Sama na Murtala Mohammed da ke Legas, CI Adeola Adeshoken, sun bayyana cewa za su miƙe tsaye domin cika aikin umarnin da CGI Isah Jere ya ba su a game da shirin hukumar na tunkarar zaɓen 2023 da sauran laifuka da suka shafi shige da fice.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: An Gargadi ‘Yan Siyasa Kan Yakin Neman Zabe A Wuraren Ibada Da Fadar Sarakuna

Next Post

Shugabannin Sin Da Argentina Sun Aike Da Wasikar Murnar Bude Dandalin Musayar Al’adu Tsakanin Kasashen Biyu

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

8 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

9 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

10 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

15 hours ago
NIS
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

15 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

16 hours ago
Next Post
Shugabannin Sin Da Argentina Sun Aike Da Wasikar Murnar Bude Dandalin Musayar Al’adu Tsakanin Kasashen Biyu

Shugabannin Sin Da Argentina Sun Aike Da Wasikar Murnar Bude Dandalin Musayar Al'adu Tsakanin Kasashen Biyu

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.