ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Zaɓe: Mun Ƙwace Katin Zaɓe Da Shaidar Ɗan Ƙasa 526 Daga ‘Yan Ƙasar Waje – Shugaban NIS

by Abdulrazaq Yahuza
4 years ago
NIS

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), CGI Isah Jere Idris ya bayyana cewa hukumarsa ta ƙwace katin zaɓe da aƙalla katin shaidar zama ɗan ƙasa 526 daga hannun baƙi ‘yan ƙasar waje a faɗin Nijeriya.

Ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabin buɗe wani taron da ya kira ɗaukacin manyan kwanturololin hukumar da ke sassa daban-daban na ƙasa domin shirin tunkarar ayyukan da hukumar za ta yi yayin gudanar da harkokin zaɓen 2023.

“Bisa tsarin jadawalin zaɓe na ƙasa, a yau (Laraba) jam’iyyu ke fara yaƙin neman zaɓe. A ƙoƙarin da muke yi na fara kimtsa jami’anmu manya da ƙanana domin tunkarar shirye-shiryen zaɓen da wuri, na gayyato Kwanturololin Manyan Ofisoshinmu na Jihohi domin mu ƙarfafa sintiri a iyakokin ƙasa a wannan lokacin. Ana sa ran su yi haɗin gwiwa da sauran hukumomi wajen hana kwararowar baƙin-haure da bazuwar ƙananan makamai wanda ka iya kawo cikas ga gudanar da zaɓe cikin kwanciyar hankali da lumana.

ADVERTISEMENT

“Bugu da ƙari za mu ruɓanya ƙoƙarinmu wajen gudanar da sintiri da sanya idanu sosai a duk faɗin ƙasar nan. Za mu yi haka ne domin tabbatar da cewa babu wani ɗan ƙasar waje da aka bari ya yi ya kaɗa ƙuri’a a zaɓen ko kuma ya haddasa fitina a wannan lokacin mai muhimmanci.” In ji shi.

  • Kotu Ta Tabbatar Da Machina A Matsayin Dan Takarar Sanatan APC A Mazabar Yobe Ta Arewa

Isah Jere ya ce hukumar ta duƙufa ka’in da na’in wajen tabbatar da cewa babu wani baƙo da aka bari ya yi katsalandan a zaɓen na 2023.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

“Tuni muka ƙwace katinan zaɓe da na shaidar zama ɗan ƙasa na NIMC. Daga bayanan da muke da su a yau, akwai katin ɗan ƙasa 526 da muka ƙwace daga ‘yan ƙasashen waje waɗanda suka mallaka ta haramtattun hanyoyi. Nan da ‘yan kwanaki masu zuwa, muna sa ran ƙwace ƙarin wasu a sassa daban-daban na ofisoshinmu da ke ƙasar nan.”

NIS
Dandazon Kwanturololin Jihohi na NIS da suka halarci taron

Wakazalika, shugaban hukumar ta NIS ya gargaɗi dukkan manyan jami’an da ke shugabantar sassan hukumar kar su kuskura su bari a haɗa baki da su don mara wa wata jam’iyya baya, yana mai cewa duk wanda aka kama da laifin hakan zai ɗanɗana kuɗarsa.

“Akwai buƙatar kwanturololi na jihohi su ƙara zage damtse a wannan lokacin wajen gudanar da ayyukansu, domin duk wani abu da aka aikata da ya saɓa wa ƙa’idar aiki akwai hukunci a kai daidai da yadda dokar aikin gwamnati ta tanada.”

Har ila yau, CGI Jere ya nemi haɗin kan ‘yan jarida wajen samun nasarar ayyukan da suke gudanarwa, domin a cewarsa, “`yan jarida kuna daga cikin masu ruwa da tsaki. Labarun da kuke tattarowa yayin gudanar da ayyukanku za su iya taimakawa gaya wajen magance matsalolin tsaron ƙasa.

“Mu a NIS, mun yi ammanar cewa haɗin gwiwa da dukkan masu ruwa da tsaki yana da matuƙar muhimmanci wajen samun nasarar ayyukanmu. A kan haka, muna maraba da duk wani abu na kishin ƙasa da za a haɗa hannu da mu a kai domin tabbatar da ci gaban ƙasar da muke fatan gani a Nijeriya.

“Ina tabbatar muku da cewa a kullum ƙofarmu a buɗe take wajen karɓar bayanai da za su taimake mu gudanar da aiki tuƙuru ga ƙasa, sannan ina kira gare ku a koyaushe ku riƙa gudanar da sahihin bincike a kan duk wani labari da kuka ji a game da mu. Wannan roƙo ne na neman adalci da muke muku saboda bai saɓa wa ƙa’idar aikin jarida ba wadda ta jaddada buƙatar yi wa kowane ɓangare adalci wajen tuntuɓa don a ji ta bakinsa. A madadin mahukuntan NIS da ɗaukacin jami’anta, muna godiya da kuka amsa gayyatarmu.” Ya bayyana.

  • https://leadership.ng/nis-unodc-unveil-report-on-migrants-smuggling/

Da suke tofa albarkacin bakinsu daban-daban, Kwanturolan NIS na Jihar Bayelsa, CI Sunday James da takwaransa na iyakar ƙasa ta Jibiya, CI Kelechi Ekeoba da kuma ta Filin Jiragen Sama na Murtala Mohammed da ke Legas, CI Adeola Adeshoken, sun bayyana cewa za su miƙe tsaye domin cika aikin umarnin da CGI Isah Jere ya ba su a game da shirin hukumar na tunkarar zaɓen 2023 da sauran laifuka da suka shafi shige da fice.

 

NIS
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Shugabannin Sin Da Argentina Sun Aike Da Wasikar Murnar Bude Dandalin Musayar Al’adu Tsakanin Kasashen Biyu

Shugabannin Sin Da Argentina Sun Aike Da Wasikar Murnar Bude Dandalin Musayar Al'adu Tsakanin Kasashen Biyu

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.