• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ina Da Karfin Jiki, Lafiyayye Ne Ni, Tinubu Ya Warware Jita-jitar Rashin Lafiya A Bidiyo

by Muhammad
3 years ago

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, daga can birnin Landan, ya shiga dandalin sada zumunta na yanar gizo ya wallafa wani bidiyonsa yana motsa jiki domin tabbatar da lafiyarsa.

A cikin wani gajeren faifan bidiyo da ya saka a daren Lahadi, an ga Tinubu akan keken motsa jiki, yana mai cewa sabanin rade-radin da ake yadawa, yana cikin koshin lafiya.

  • Tinubu: Jonathan Ba Zai Kubutar Da Kai A Zaben 2023 Ba —PDP
  • An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

Tinubu dai ya bar Nijeriya zuwa kasar Ingila, lamarin da ya haifar da cece-ku-ce a kan cewa tafiyar tasa ba za ta rasa nasaba da rashin lafiya mai tsanani ba, musamman ma a lokacin da ya fito fili a lokacin rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da daukacin ‘yan takarar shugaban kasa da jam’iyyunsu suka yi.

Amma a cikin faifan bidiyon, wanda ya wallafa a shafin sa na Twitter da aka tabbatar, Tinubu ya kuma bar wani takaitaccen sako, yana mai cewa, “Da yawa sun ce na mutu; wasu kuma na cewa na janye daga yakin neman zaben shugaban kasa. To… a’a.

“Wannan ita ce gaskiya: Ina da ƙarfin jiki, ina cikin koshin lafiya kuma a shirye nake na bauta wa ‘yan Nijeriya tun daga ranar farko da na zama shugaban kasa.”

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Sakamakon rahotannin da ake zarginsa da rashin lafiyarsa, kungiyar yakin neman zaben jam’iyyar APC ta karyata jita-jitar, tare da nuna cewa Tinubu na cikin koshin lafiya.

Da yake mayar da martani ga wani hoton bogi da ya karade kafafen sada zumunta da ke nuna cewa Tinubu ba shi da lafiya, daraktan yada labarai da wayar da kan jama’a na kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bayo Onanuga, ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa: “Ku kalli tagar gilashin sa. Bari in tabbatar wa ‘yan Nijeriya masu son sanin inda Tinubu yake. Yana Landan, a gidansa.

“Tinubu ya bar Nijeriya ne a daren ranar Asabar don hutu da kuma shirye-shiryen yakin neman zabe.

“Na gan shi na yi magana da shi sa’o’i biyu kafin ya tafi. Yana da hazaka da tausayi. lafiyarsa garau. Bai je jinyar wata cuta ba.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu
Siyasa

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027
Siyasa

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu
Siyasa

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Next Post
Ganduje Ya Jajantawa Shugaban KAROTA Baffa DanAgundi Sakamakon Rasuwar Mahaifiyarsa

Ganduje Ya Jajantawa Shugaban KAROTA Baffa DanAgundi Sakamakon Rasuwar Mahaifiyarsa

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.