ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

Sunan Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yi Batan-dabo Cikin Kwamitin

by Khalid Idris Doya
4 years ago
PDP

An nada mamba kuma jigo a jam’iyyar PDP sannan Sanatan da ke wakiltar mazabar Enugu ta Gabas, Chimaroke Nnamani a cikin kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023 da ke karatowa.

Hakan na kunshe cikin jerin sunayen da aka fitar a daren ranar Juma’a inda aka nemi sunan mataimain shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo sama da kasa cikin jerin kwamitin yakin zaben na Tinubu aka rasa, inda aka rawaito cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya umarci mataimakin nasa da ya maida hankali kawai wajen gudanar da mulki.

  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS
  • Dakarun Kasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Wanzar Da Zaman Lafiya

Kazalika, jam’iyyar ta ki sanya sunan tsohon kakakin majalisar dokokin tarayya, Yakubu Dogara, tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal; tsohon ministan ilimi, Chukwuemeka Nwajiuba da dan-gani-kashenin Tinubu, Adebayo Shittu, wadda ya jagoranci manyan kungiyoyin goyon bayan Tinunu, ‘Asiwaju Tinubu-Shettima Coalition for Good Governance’ dukka babu sunayensu.

ADVERTISEMENT

A wata sanarwar da jami’in watsa labarai na kwamitin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, Festus Keyamo (SAN) ya fitar, ya ce an cire sunan Osianbajo da sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha daga cikin kwamitin yakin zaben ne sakamakon umarnin da shugaba Buhari ya bayar na cewa su maida hankali wajen gudanar da harkokin mulkin Nijeriya a halin yanzu.

Jerin kwamitin yakin zaben mai mutum 422 da sakataren kwamitin yakin zaben, Hon. James Faleke ya fitar, kuma an gano cewa wasu jerin fitattun jigogin jam’iyyar babu sunayensu a ciki.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kazalika, shugaba Muhammadu Buhari shine shugaban kwamitin yakin zaben, Bola Ahmed Tinubu kuma shine mataimakin shugaba na kwamitin yakin zaben APC, yayin da kuma gwamnan jihar Filato, Simon Bako Lalong ya kasance darakta-janar yakin neman zabe na Tinubu.

Tsohon shugaban jam’iyyar, Kwamared Adams Oshiomhole shine aka ayyana a matsayin mataimakin darakta-janar nay akin zaben a sashin ayyuka, sanna akwai sunayen gwamnoni, ministoci, ‘yan majalisu, jakadu, da wasu jiga-jigai cikin kwamitin yakin zaben na Tinubu.

A sanarwar ta Keyamo, ya ce sabanin yadda wasu rahotonni ke yawo na cewa an cire sunayen wasu na kusa-kusan Buhari cikin kwamitin yakin zaben da kokarin nuna cewa akwai Baraka a jam’iyyar, ya ce sam ba haka zancen yake ba, illa dai ya nuna cewa Buhari ne ya umarci Osinbajo da Boss da su maida hankali wajen gudanar da mulki.

“A matsayin jam’iyyar da ta san meye take yi da gwamnatin da ta san meye take yi, ba zai yiyu a kwashe dukkanun manyan jami’an gwamnati a ce su bar ayyukansu su shiga kwamitin yakin zabe ba. APC ita ce ke da ikon jan ragamar Nijeriya har zuwa ranar 29 ga watan Mayun 2023, don haka akwai bukatar wasu su fi maida hankali wajen gudanar da harkokin mulki ba zallar yakin zabe ba.”

PDP
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta
Manyan Labarai

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

July 3, 2026
Next Post
Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar

July 5, 2026
Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano

Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano

July 5, 2026
Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

July 5, 2026
Zulum Ya Bayar Da Cak Na Naira Biliyan 5.81 Domin Biyan Bashin Garatutin Ma’aikata Masu Ritaya

Zulum Ya Bayar Da Cak Na Naira Biliyan 5.81 Domin Biyan Bashin Garatutin Ma’aikata Masu Ritaya

July 5, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 5, 2026
Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

July 5, 2026
Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

July 5, 2026
Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.