• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Sauran Rina A Kaba A Kokarin Masu Ruwa Da Tsakin Jam’iyyar PDP Na Shawo Kan Wike

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Wike

A kokarin lalibowa da nemo mafita ta karshe kan rikicin da ke faruwa a cikin jam’iyyar PDP, mambobin Majalisar amintattu na jam’iyyar sun gana da gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike, a gidan gwamnati da ke Fatakwal a ranar Talata.

Da yake magana bayan kammala ganawar sirri da suka yi tare da gwamnan, mai rikon mukamin Shugaban Majalisar amintattu na jam’iyyar kuma tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Adolphus Wabara, ya ce, ganawar ta gudana cikin kwankiyar hankali amma dai ba kammalata ba tukunna, inda ya ayyana ta a matsayin ‘Inkunkulusib’.

  • Kwamitin Amintattu Na PDP Ya Gana Da Wike Kan Rikicin Jam’iyyar

Wabara ya ce: “Mun kwashe sama da awanni hudu muna tattaunawa da hazikin gwamna na jihar Ribas. Mun shafe sama da awa hudu amma ba a kammala ganawar ba.

“Kun san tabbatar da zaman lafiya na iya daukan lokaci. Amma, Ina tunanin mun kusa cimma gaci. Mun na da kwarin guiwa. Mun ji bangaren gwamnan. Za mu koma Abuja mu hado duk abubuwan da muka tattaro.

“Ganawarmu ta yi armashi, amma wani abu guda da nake son kowa ya sani shine wannan ahlin za ta ci gaba da zama gida daya a lema daya wato PDP, kuma da izinin Allah za mu kai ga kammalawa cikin nasara. Tare da hadin kai shi (Wike) da sauran dukkanin Gwamnoni za mu kai mataki na gaba.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Ya nuna kwarin guiwarsa na cewa nan kusa kadan za su shawo kan matsalolin tare da tabbatar da cewa PDP ta Kara zama a karkashin lema daya domin tunkarar abubuwan da suke gabanta.

Ya kara da cewa a daidai lokacin da gangamin yakin neman zaben na shugaba kasa ya kankama, jam’iyyar za ta tabbatar dukkanin abubuwan da suka kamata suna layin da ya dace domin kai jam’iyyar ga nasara.

Da yake ganawa da ‘yan jarida, gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike, ya ce, abu mai matukar muhimmanci shine PDP tana dinke wuri guda.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu
Siyasa

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Next Post
‘Yan Takarar PDP Sun Maka Ayu, Anyanwu Da Wasu A Komar EFCC Kan Zargin Badakalar Kudade

'Yan Takarar PDP Sun Maka Ayu, Anyanwu Da Wasu A Komar EFCC Kan Zargin Badakalar Kudade

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

October 16, 2025
An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.