ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Sauran Rina A Kaba A Kokarin Masu Ruwa Da Tsakin Jam’iyyar PDP Na Shawo Kan Wike

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Wike

A kokarin lalibowa da nemo mafita ta karshe kan rikicin da ke faruwa a cikin jam’iyyar PDP, mambobin Majalisar amintattu na jam’iyyar sun gana da gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike, a gidan gwamnati da ke Fatakwal a ranar Talata.

Da yake magana bayan kammala ganawar sirri da suka yi tare da gwamnan, mai rikon mukamin Shugaban Majalisar amintattu na jam’iyyar kuma tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Adolphus Wabara, ya ce, ganawar ta gudana cikin kwankiyar hankali amma dai ba kammalata ba tukunna, inda ya ayyana ta a matsayin ‘Inkunkulusib’.

  • Kwamitin Amintattu Na PDP Ya Gana Da Wike Kan Rikicin Jam’iyyar

Wabara ya ce: “Mun kwashe sama da awanni hudu muna tattaunawa da hazikin gwamna na jihar Ribas. Mun shafe sama da awa hudu amma ba a kammala ganawar ba.

ADVERTISEMENT

“Kun san tabbatar da zaman lafiya na iya daukan lokaci. Amma, Ina tunanin mun kusa cimma gaci. Mun na da kwarin guiwa. Mun ji bangaren gwamnan. Za mu koma Abuja mu hado duk abubuwan da muka tattaro.

“Ganawarmu ta yi armashi, amma wani abu guda da nake son kowa ya sani shine wannan ahlin za ta ci gaba da zama gida daya a lema daya wato PDP, kuma da izinin Allah za mu kai ga kammalawa cikin nasara. Tare da hadin kai shi (Wike) da sauran dukkanin Gwamnoni za mu kai mataki na gaba.”

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Ya nuna kwarin guiwarsa na cewa nan kusa kadan za su shawo kan matsalolin tare da tabbatar da cewa PDP ta Kara zama a karkashin lema daya domin tunkarar abubuwan da suke gabanta.

Ya kara da cewa a daidai lokacin da gangamin yakin neman zaben na shugaba kasa ya kankama, jam’iyyar za ta tabbatar dukkanin abubuwan da suka kamata suna layin da ya dace domin kai jam’iyyar ga nasara.

Da yake ganawa da ‘yan jarida, gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike, ya ce, abu mai matukar muhimmanci shine PDP tana dinke wuri guda.

Wike
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
‘Yan Takarar PDP Sun Maka Ayu, Anyanwu Da Wasu A Komar EFCC Kan Zargin Badakalar Kudade

'Yan Takarar PDP Sun Maka Ayu, Anyanwu Da Wasu A Komar EFCC Kan Zargin Badakalar Kudade

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026
Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Sanata yari

Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari

September 11, 2026
Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 11, 2026
SAW

Ɗabi’un Annabi (SAW) Kan Abubuwa Na Al’adar Rayuwa

September 11, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

September 11, 2026
Wike

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

September 11, 2026
Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Wike

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.