• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Kungiya Ta Yi Barazanar Maka Kungiyar Kwadago A Kotu A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Wata Kungiya Ta Yi Barazanar Maka Kungiyar Kwadago A Kotu A Jihar Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kungiya mai suna ‘Democracy Defenders Forum’, ta yi barazanar maka Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC), reshen Jihar Kebbi a gaban kotu kan gangamin goyon bayan wani dan takarar gwamna a jihar.

Shugaban kungiyar Almustapha Habib-Yauri ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

  • Zan Daukaka Kara Kan Hukuncin Kotu Da Ya Soke Takarata – Aisha Binani
  • ICPC Ta Rufe Makarantu 68 Na Bogi A Nijeriya

Ya ce: “Majalisar ta lura da takaicin takardar da ake yadawa da ake zargin ta fito ne daga kungiyar kwadago, reshen Jihar Kebbi, inda ta gayyaci kungiyoyin siyasa da daidaikun mutane zuwa wani gangami a ranar Talata, 25 ga Oktoba, 2022.

“Taron na nuna goyon baya ne ga Nasiru Idris, dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zabe mai zuwa a jihar.”

Habib-Yauri ya ce saboda haka kungiyar ta yi Allah wadai da irin wannan mataki gaba daya, sanin cewa bai dace da dokokin da suka kafa kungiyar ba.

Labarai Masu Nasaba

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

“Ba mu ci karo da dokokin Nijeriya masu tsayuwa da suka ba da damar ’yancin yin tarayya da jama’a, ciki har da ‘yancin ma’aikata dangane da matsayinsu na siyasa amma ba wai goyon bayan shugabanni na ja da kungiyar a matsayinta na jam’iyya ba.

“Don haka muna kira ga shugabannin kungiyar NLC a jihar da su tabbatar da irin wannan gayyata da ake yadawa tare da yin bayani karara kan hannu ko akasin haka cikin kankanin lokaci,” in ji shi.

Shugaban ya ci gaba da cewa “Idan har kungiyar kwadago ta NLC ta amince da sa hannunta kuma ta ci gaba da aiwatar da irin wannan shiri, za a bar dandalin ba tare da wani zabin da ya wuce maka kungiyar NLC a kotun sauraren kararrakin ma’aikata.

“Kamar yadda muke la’akari ba wai kawai yunkurin da bai dace ba ne amma yunkurin lalata martabar kungiyar kwadago ta Nijeriya da sauran kungiyoyin da ke da alaka da su zai yi, inji shi.”

Da aka tuntubi shugaban NLC reshen Jihar Kebbi, Umar Alhassan-Halidu ya ce: “ Kungiyar za ta gudanar da taron majalisar koli ta kasa a Jihar kebbi a ranar Talata, 24 ga Oktoba.

“Washegari da safe za mu yi tattaki (taron gangami) zuwa filin wasa na Haliru Audu, Nasiru Idris Kauran Gwandu na cikinmu, shi ne mataimakin shugaban NLC na kasa, dole ne mu nuna masa hadin kai da goyon bayan takararsa.

“Idan za a tuna lokacin da Adams Oshomole ya tsaya takara haka aka yi masa a matsayinsa na tsohon shugaban NLC, babu wani sabon abu, a matsayinmu na ma’aikata mu ma muna da jam’iyyarmu, mun yi rajistar Labour Party (LP) don kawai ma’aikatan Nijeriya su samu jam’iyyarsu kuma mun dauki nauyin jam’iyyar, in ji shi.

“A matsayinmu na ma’aikata, ba za mu iya yin zaman banza ba, dole ne mu shiga harkokin siyasa domin mu ma ‘yan Nijeriya ne.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GangamiJihar KebbiKotuKungiyaNlcSiyasaTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kogi Ta Maka Dangote A Kotu Kan Takaddamar Kamfanin Simintin Obajana

Next Post

Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

Related

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

58 minutes ago
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

5 hours ago
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
Manyan Labarai

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

7 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

20 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

1 day ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

1 day ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

LABARAI MASU NASABA

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

July 2, 2025
Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

July 2, 2025
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

July 2, 2025
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

July 2, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

July 2, 2025
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.