ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Kungiya Ta Yi Barazanar Maka Kungiyar Kwadago A Kotu A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
4 years ago
Kungiyar Kwadago

Wata kungiya mai suna ‘Democracy Defenders Forum’, ta yi barazanar maka Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC), reshen Jihar Kebbi a gaban kotu kan gangamin goyon bayan wani dan takarar gwamna a jihar.

Shugaban kungiyar Almustapha Habib-Yauri ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

  • Zan Daukaka Kara Kan Hukuncin Kotu Da Ya Soke Takarata – Aisha Binani
  • ICPC Ta Rufe Makarantu 68 Na Bogi A Nijeriya

Ya ce: “Majalisar ta lura da takaicin takardar da ake yadawa da ake zargin ta fito ne daga kungiyar kwadago, reshen Jihar Kebbi, inda ta gayyaci kungiyoyin siyasa da daidaikun mutane zuwa wani gangami a ranar Talata, 25 ga Oktoba, 2022.

ADVERTISEMENT

“Taron na nuna goyon baya ne ga Nasiru Idris, dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zabe mai zuwa a jihar.”

Habib-Yauri ya ce saboda haka kungiyar ta yi Allah wadai da irin wannan mataki gaba daya, sanin cewa bai dace da dokokin da suka kafa kungiyar ba.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

“Ba mu ci karo da dokokin Nijeriya masu tsayuwa da suka ba da damar ’yancin yin tarayya da jama’a, ciki har da ‘yancin ma’aikata dangane da matsayinsu na siyasa amma ba wai goyon bayan shugabanni na ja da kungiyar a matsayinta na jam’iyya ba.

“Don haka muna kira ga shugabannin kungiyar NLC a jihar da su tabbatar da irin wannan gayyata da ake yadawa tare da yin bayani karara kan hannu ko akasin haka cikin kankanin lokaci,” in ji shi.

Shugaban ya ci gaba da cewa “Idan har kungiyar kwadago ta NLC ta amince da sa hannunta kuma ta ci gaba da aiwatar da irin wannan shiri, za a bar dandalin ba tare da wani zabin da ya wuce maka kungiyar NLC a kotun sauraren kararrakin ma’aikata.

“Kamar yadda muke la’akari ba wai kawai yunkurin da bai dace ba ne amma yunkurin lalata martabar kungiyar kwadago ta Nijeriya da sauran kungiyoyin da ke da alaka da su zai yi, inji shi.”

Da aka tuntubi shugaban NLC reshen Jihar Kebbi, Umar Alhassan-Halidu ya ce: “ Kungiyar za ta gudanar da taron majalisar koli ta kasa a Jihar kebbi a ranar Talata, 24 ga Oktoba.

“Washegari da safe za mu yi tattaki (taron gangami) zuwa filin wasa na Haliru Audu, Nasiru Idris Kauran Gwandu na cikinmu, shi ne mataimakin shugaban NLC na kasa, dole ne mu nuna masa hadin kai da goyon bayan takararsa.

“Idan za a tuna lokacin da Adams Oshomole ya tsaya takara haka aka yi masa a matsayinsa na tsohon shugaban NLC, babu wani sabon abu, a matsayinmu na ma’aikata mu ma muna da jam’iyyarmu, mun yi rajistar Labour Party (LP) don kawai ma’aikatan Nijeriya su samu jam’iyyarsu kuma mun dauki nauyin jam’iyyar, in ji shi.

“A matsayinmu na ma’aikata, ba za mu iya yin zaman banza ba, dole ne mu shiga harkokin siyasa domin mu ma ‘yan Nijeriya ne.”

Kungiyar Kwadago
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.