ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Kungiya Ta Yi Barazanar Maka Kungiyar Kwadago A Kotu A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
4 years ago
Kungiyar Kwadago

Wata kungiya mai suna ‘Democracy Defenders Forum’, ta yi barazanar maka Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC), reshen Jihar Kebbi a gaban kotu kan gangamin goyon bayan wani dan takarar gwamna a jihar.

Shugaban kungiyar Almustapha Habib-Yauri ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

  • Zan Daukaka Kara Kan Hukuncin Kotu Da Ya Soke Takarata – Aisha Binani
  • ICPC Ta Rufe Makarantu 68 Na Bogi A Nijeriya

Ya ce: “Majalisar ta lura da takaicin takardar da ake yadawa da ake zargin ta fito ne daga kungiyar kwadago, reshen Jihar Kebbi, inda ta gayyaci kungiyoyin siyasa da daidaikun mutane zuwa wani gangami a ranar Talata, 25 ga Oktoba, 2022.

ADVERTISEMENT

“Taron na nuna goyon baya ne ga Nasiru Idris, dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zabe mai zuwa a jihar.”

Habib-Yauri ya ce saboda haka kungiyar ta yi Allah wadai da irin wannan mataki gaba daya, sanin cewa bai dace da dokokin da suka kafa kungiyar ba.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

“Ba mu ci karo da dokokin Nijeriya masu tsayuwa da suka ba da damar ’yancin yin tarayya da jama’a, ciki har da ‘yancin ma’aikata dangane da matsayinsu na siyasa amma ba wai goyon bayan shugabanni na ja da kungiyar a matsayinta na jam’iyya ba.

“Don haka muna kira ga shugabannin kungiyar NLC a jihar da su tabbatar da irin wannan gayyata da ake yadawa tare da yin bayani karara kan hannu ko akasin haka cikin kankanin lokaci,” in ji shi.

Shugaban ya ci gaba da cewa “Idan har kungiyar kwadago ta NLC ta amince da sa hannunta kuma ta ci gaba da aiwatar da irin wannan shiri, za a bar dandalin ba tare da wani zabin da ya wuce maka kungiyar NLC a kotun sauraren kararrakin ma’aikata.

“Kamar yadda muke la’akari ba wai kawai yunkurin da bai dace ba ne amma yunkurin lalata martabar kungiyar kwadago ta Nijeriya da sauran kungiyoyin da ke da alaka da su zai yi, inji shi.”

Da aka tuntubi shugaban NLC reshen Jihar Kebbi, Umar Alhassan-Halidu ya ce: “ Kungiyar za ta gudanar da taron majalisar koli ta kasa a Jihar kebbi a ranar Talata, 24 ga Oktoba.

“Washegari da safe za mu yi tattaki (taron gangami) zuwa filin wasa na Haliru Audu, Nasiru Idris Kauran Gwandu na cikinmu, shi ne mataimakin shugaban NLC na kasa, dole ne mu nuna masa hadin kai da goyon bayan takararsa.

“Idan za a tuna lokacin da Adams Oshomole ya tsaya takara haka aka yi masa a matsayinsa na tsohon shugaban NLC, babu wani sabon abu, a matsayinmu na ma’aikata mu ma muna da jam’iyyarmu, mun yi rajistar Labour Party (LP) don kawai ma’aikatan Nijeriya su samu jam’iyyarsu kuma mun dauki nauyin jam’iyyar, in ji shi.

“A matsayinmu na ma’aikata, ba za mu iya yin zaman banza ba, dole ne mu shiga harkokin siyasa domin mu ma ‘yan Nijeriya ne.”

Kungiyar Kwadago
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.