• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ainihin Ma’anar Farfado Da Kasar Sin A Sabon Zamani

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ainihin Ma’anar Farfado Da Kasar Sin A Sabon Zamani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga duk mai bibiyar yadda babban taron wakilan JKS na 20 ke gudana, ba zai gaza jin jimlar “farfado da kasar Sin daga dukkanin fannoni a sabon zamani da ake ciki” ba, musamman cikin rahoton da shugaban kasar, kuma babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping ya gabatar, wanda hakan buri ne na raya kasar da JKS ta sha alwashin cimmawa.

A karkashin wannan manufa, akwai muhimman matakai masu dacewa da salon gurguzu mai sigar musamman da kasar Sin ke bi, wanda ya tanadi samarwa al’ummar Sinawa yanayin rayuwa mai cike da zaman lafiya da wadata, da zamanantar da tattalin arziki da zamantakewa, da bunkasa al’adu, da kyautata alakar rayuwa tsakanin bil adama da sauran halittu, wadanda sakamakon su zai amfani dukkanin sassan alummun kasar ba wai wasu mutane kalilan ba.

  • Tsarin Zamanintar Da Aikin Noma Na Sin Ya Gaggauta Bunkasuwarta Da Ma Duniya Baiki Daya

Idan muka kalli wannan salon samar da ci gaba na kasar Sin, za mu ga ya sha banban da na kasashen yamma masu bin salon jari-hujja, wadanda tarihi ya jima da sanin su, a matsayin masu amfani da karfin tuwo, da mulkin mallaka wajen fadada tasirinsu a duniya, da cimma muradun kashin kai ta kowace irin hanya.

Ko shakka babu, salon gurguzu mai halayyar musamman na Sin, ya haifar da babbar dama ta yakar talauci, inda karkashinsa kasar ta cimma nasarar tsamo al’ummarta da yawansu ya kusa miliyan 100 daga kangin talauci cikin shekaru 10 kacal, matakin da masu fashin baki ke ganin ya shiga tarihin duniya, a matsayin irin wanda ba a taba gani ba a shekarun baya bayan nan.

Alal hakika, JKS ta dora muhimmancin gaske ga moriyar al’ummar Sinawa. Jam’iyya ce da har kullum ke aiki tukuru, wajen ganin ba a bar wani rukuni na al’umma a baya ba a dukkanin fannonin ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Ana kuma iya ganin hakan a zahiri, idan aka yi duba ga bangarorin da kasar Sin ta cimma manyan nasarori a cikinsu, kamar bunkasar tattalin arziki, da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da fadadar fannin ilimin kimiyya da fasaha, da karuwar guraben ayyukan yi, da tsara manufofin inganta rayuwar tsofaffi da yara kanana da sauran su.

Tabbas wannan kadan ne daga ainihin ma’anar matakan farfado da kasar Sin a sabon zamani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Tsaro Sun Kashe ‘Yan Ta’addar Da Suka Addabi Mutane A Hanyar Abuja-Kaduna

Next Post

Kasar Sin Ba Za Ta Sauya Niyyarta Ta Habaka Bude Kofa Ga Kasashen Waje Ba

Related

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

13 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

14 hours ago
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

15 hours ago
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma
Daga Birnin Sin

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

16 hours ago
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5
Daga Birnin Sin

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

17 hours ago
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

19 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ba Za Ta Sauya Niyyarta Ta Habaka Bude Kofa Ga Kasashen Waje Ba

Kasar Sin Ba Za Ta Sauya Niyyarta Ta Habaka Bude Kofa Ga Kasashen Waje Ba

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

July 3, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3

July 3, 2025
Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

July 3, 2025
Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.