ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
Rasha

Yayin wani faretin soji a birnin Beijing, makamai masu linzami rundunar sojin China ta People’s Liberation Army na wucewa a hankali rataye a kan manyan motoci masu launin kakin soji.

Makaman masu tsawon mita 11 da nauyin tan 15, kowannensu na dauke da kalmomi da lambobi na “DF-17”.

  • Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund
  • Xi Ya Gana Da Shugaban Jam’iyyar United Russia 

A wannan lokacin ne China ta kaddamar wa duniya da sabon makaminta Dongfeng mai linzami mai gudun walkiya wanda ake kira hypersonic a Turance.

ADVERTISEMENT

An yi hakan ne ranar 1 ga watan Oktoban 2019.

Da ma Amurka na sane da shirin na China, amma kuma tuni Chinar ta ci gaba da inganta makaman tun daga lokacin.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Saboda tsabar gudunsu da kuma zilliya inda suke da sauri ninki biyar na gudun sauti makamai ne da ka iya sauya yadda ake fafata yaki a yanzu.

Hakan ta sa yanzu kasashe ke rige-rigen samar da su.

Rasha, China, Amurka: rigegeniyar nuna iko Bikin faretin na Beijing ya jawo rade-radi game da barazanar da China ke yi wa kasashen Yamma da makamanta masu linzami. Yanzu ita ce kan gaba wajen samar da su, sai kuma Rasha da ke biye mata.

Amurka kuma, na kokarin kamo su ne, yayin da Birtaniya kuma ba ta da su.

William Freer, wani mai nazarin harkokin tsaro a cibiyar Council on Geostrategy, na ganin dalilin da ya sa Rasha da China suka zarce saura abu ne mai sauki.

“Sun yanke shawarar zuba kudade masu yawa a wadannan fannonin tun shekaru baya.”

A gefe guda kuma, kasashen Yamma sun fi mayar da hankali tun daga shekara 20 da suka wuce wajen yaki da masu ikirarin jihadi a gida da kuma kasashen waje.

A lokacin, yiwuwar gwabza yaki tsakanin manyan kasashe masu karfin soji iri daya ba ta da yawa.

Aikin gwajin wani makami mai linzami mai matsakaicin nisa a Koriya ta Arewa

“Abin da ya faru shi ne, mun gaza wajen lura da barazanar China wajen inganta rundunar sojinta,” kamar yadda Sir Aled Younger, wanda ya bar mukamin shugaban hukumar tattara bayanan sirri ta Birtaniya a 2020, ya bayyana.

Sauran kasashe na ta kokari su ma: Isra’ila na da makamin hypersonic mai suna Arrow 3 wanda aka kirkira domin kakkabo makamai.

Iran ta yi ikirarin cewa tana da shi, wanda ta ce ta harba wa Isra’ila lokacin yakin kwana 12 da suka gwabza a watan Yuni.

(Tabbas makamin ya yi gudun walkiya amma ba a tunanin yana da ikon zilliya mai yawa da za a kira shi cikakken hypersonic).

Koriya ta Arewa ma na ta yin aiki kan nata tun 2021, har ma ta yi ikirarin cewa tana da makamin.

Yanzu Amurka da Birtaniya na zuba kudade a fannin makaman hypersonic, kamar yadda saura kamar Japan da Faransa ke yi.

Amurka ta kaddamar da nata makamin mai gudun hypersonic mai suna “Dark Eagle”.

Amma dai a yanzu China da Rasha ne kan gaba sosai, inda wasu masana a kasashen Yamma ke cewa abin damuwa ne.

Dankaren gudu da mummunar barna

Kalmar hypersonic na nufin wani abu mai gudun tsiya kan ma’aunin March 5 ko sama da haka. Ma’ana mai gudu ninki biyar na sauti ko kuma gudun mil 3,858 cikin awa daya.

Wannan gudun nasu shi ne abin da ya sa ake fargaba game da su.

Makamin da aka sani mafi gudu zuwa yanzu shi ne na Rasha mai suna Abangard – wanda aka ce ya kan yi gudun Mach 27 (kusan mil 20,700 cikin awa daya), kodayake an fi ambato gudun Mach 12.

Game da barnar da suke haifarwa, irin wadannan makaman ba su fi sauran makamai masu linzami hadari mai yawa ba, a cewar Mista Freer.

“Wahalar ganowa da kuma kakkabo su ce ke sakawa ana tsoronsu sosai.”

Akan harba su ne da taimakon wata roka, idan suka kai kololuwar tashi sai kuma su shiga wani yanayi da ake kira “scramjet engine” wanda shi kuma zai yi musu jagora domin dira inda aka aika su.

Akan yi amfani da su ta hanya biyu, ma’ana bam din suke dauke da shi zai iya zama na nukiliya ko kuma gama-garin bam.

Kafin a ayyana makami a matsayin mai gudun walkiya na hypersonic, dole ne sai ya mallaki ikon zillewa makaman kariya. Wanda ya harba shi zai dinga sassauya masa hanyar tafiya ta yadda abokin gabarsa ba zai iya gane shi ba har sai ya dira kan wurin da ya nufa.

“Ta hanyar kauce wa nau’rorin leken samaniya, sukan kauce wa abokan gaba har sai lokacin da suke dab da isa wanda hakan zai sa babu damar da za a iya tare su,” Patrycja Bazylczyk, mai bincike a sashen Missile Defence Project na cibiyar Centre for Strategic and International Studies da ke Amurka.

Rasha
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

MASU ALAKA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
Kasashen Ketare

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
Kasashen Ketare

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Next Post
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

LABARAI MASU NASABA

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.