• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Kama Wasu ’Yan Kwaya 4 Da Ake Nema Ruwa A Jallo Kan Mu’amala Da Miyagun Kwayoyi

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
NDLEA Ta Kama Wasu ’Yan Kwaya 4 Da Ake Nema Ruwa A Jallo Kan Mu’amala Da Miyagun Kwayoyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA), ta kama wasu mata biyu da wasu maza biyu da ake nema ruwa a jallo bisa zarginsu da laifin safarar miyagun kwayoyi sama da kilogiram 16,000 da aka kama a Legas, Abuja da kuma Netherlands.

Kakakin hukumar NDLEA, Femi Babafemi, ya ce a Legas jami’an yaki da muggan kwayoyi sun shafe makonni suna bin diddigin, Aro Aderinde mai shekaru 48, sun kama shi a ranar Lahadi 16 ga watan Oktoba, bisa zarginsa da hannu wajen fitar da tabar wiwi kilogiram 3,149 da aka boye a cikin kwakwa, mai lambar kwantena MSKU 1820587.

  • NDLEA Ta Damke Mutum 345 Bisa Zargin Ta’ammali Da Miyagun Kwayoyi A Katsina
  • NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu Da Dalibin Jami’a Kan Safarar Miyagun Kwayoyi

Haka kuma, an kama wasu mata biyu: Hauwawu Bashiru da Basirat Adebisi Yahaya kan yunkurin fitar da kilogiram 90 na methamphetamine zuwa kasashen waje ta hannun Fasto Anietie Okon Effiong na Cocin Promise of Zion Church, Oron, jihar Akwa Ibom, kamar yadda aka kama a Legas kuma aka koma Uyo don fuskantar tuhuma tare da limamin cocin.

Ku tuna cewa tun farko an kama Fasto Effiong a ranar Asabar 6 ga Agusta, 2022.

Wani da ake zargi da laifin safarar miyagun kwayoyi, Abdulkadir Mohammed, mai shekaru 47, wanda ake nema ruwa a jallo bisa kama shi da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 5,640 a wani dakin ajiya da ke unguwar Chukuku a Kuje, Abuja, a ranar Lahadi 16 ga watan Oktoba, bayan kama matarsa, Saadatu Abdullahi, mai shekaru 35, wadda ta kasance an same shi a kantin lokacin da aka kai samamen.

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

A halin da ake ciki kuma, an kama wani fitaccen mai sayar da magunguna a unguwar Mushin-Isolo ta Legas, Monday Michael, mai shekaru 45, a ranar Litinin 17 ga watan Oktoba, yayin da gano jigilar kilogiram 365.7 na tabar wiwi a cikin motoci kirar Toyota Sienna guda biyu masu lamba FST 189 FD da FST 273 GF.

A jihar Edo, an kama akalla mutane 10 da ake zargi da hannu wajen kama tabar wiwi mai nauyin kilogiram 4,870.2 a sassan jihar.

A ranar Laraba 19 ga watan Oktoba, jami’an tsaro sun kai farmaki kan iyakar dajin Ohusu, karamar hukumar Ovia ta kudu maso yammacin kasar inda suka kwato jimillar kilogiram 3,159.7 tare da kama mutane uku: Effiong Udo; Daniel Asuquo Ebong da Asuquo Effiong.

Hakazalika, a ranar Asabar, 22 ga watan Oktoba, jami’an ‘yan sanda sun kama wata motar kirar Toyota Sienna ta sararin samaniya dauke da buhu 49 na C/S mai nauyin kilogiram 638.5 a kan titin Owenusi a karamar hukumar Uhunmonde, yayin da aka kwato kilo 36 na abu daya da aka ajiye a cikin daji dake kan titin Uromi/Ubiaja.

A wani farmakin kuma an kama mutane uku da ake zargi da suka hada da John Paul, Liberty Rolland, da Aboki Stephen a Okpe da ke Akoko Edo dauke da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 55.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Karramawar Shugaban Kasa Ta Kara Min Ƙaimi – Sadiya Farouq

Next Post

Xi Ya Jaddada Fa’idar Babban Taron Wakilan JKS Na 20

Related

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

5 hours ago
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
Labarai

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

6 hours ago
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
Labarai

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

7 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

9 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

11 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

11 hours ago
Next Post
Xi Ya Jaddada Fa’idar Babban Taron Wakilan JKS Na 20

Xi Ya Jaddada Fa’idar Babban Taron Wakilan JKS Na 20

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.