ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu Da Dalibin Jami’a Kan Safarar Miyagun Kwayoyi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
NDLEA

Hukumar dakile safaran miyagun kwayoyi (NDLEA) ta cafke wata mata mai juna biyu da wata uwa mai jego da wata dalibar jami’a ‘yar aji biyu kan safaran miyagun kwayoyi.

Hukumar ta NDLEA ta ce, wadanda ake zargin su na daga cikin mutum 28 ne da ta kama da tabar Wiwi mai nauyin kilogiram 9,437.7 da tabulet din maganin opioids da sauran miyagun kwayoyi a samamen da ta gudanar a jihohin 12 da suka kunshi: Yobe, Ondo, Edo, Rivers, Akwa Ibom, Imo, Jigawa, Kogi, Adamawa, Kaduna, Kwara, Lagos da kuma babban birnin tarayya Abuja.

  • NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu, Uwa Mai Shayarwa Da Dalibar Jami’a Kan Safaran Miyagun Kwayoyi

Kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi a FCT, ya ce, dakarunsu a ranar Asabar 15 ga watan Oktoba sun mamayi wani kauye mai suna Chukuku, mai nisan kilomita 10 da Gwagwalada inda suka gano wani katafaren rumbun boye tabar Wiwi.

ADVERTISEMENT

Inda aka kamo jumbo 510 na haramtattun tabar masu nauyin kilogiram 5, 640 tare da cafke wata mata mai shayarwa Sa’adatu Abdullahi, ‘yar shekara 35, da take kula da rumbun.

A jihar Yobe kuwa hukumar ta kama kilograms na tabar Wiwi 48 a Buni Yadi, kuma sun mamayi wani wuri da ke Potiskum inda suka kamo kilograms na tabar 31 daga wajen mutum biyu da ake zargi Mohammed Mamuda da wata matar aure mai juna biyu, Hauwa Haruna.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Kazalika, wata dalibin jami’ar karatu daga gida (NOUN) da ke karanta ilimin aikin jarida, Ms. Mercy Nyong, ‘yar shekara 30 a duniya, a ranar Laraba 12 ga watan Oktaba.ne ta fada tarkon hukumar a filin sauka da tashi na Jirgin saman kasa da kasa ta Murtala Muhammad da ke Ikeja, Legas a kokarinta na fita da garam 300 na Tramadol samfurin 225mg cikin abun boye turare zuwa Dubai.

Sannan wasu ‘yan kasar Ghana su 9 an cafke su a kokarinsu na yin safaran kilograms 10,843.95 na tabar Wiwi ta tekun Nijeriya, inda kuma a ranar Juma’a 14 ga watan Oktoba aka yanke musu hukuncin zaman gidan yari na shekara 72.

Da fari dai jami’an hukumar tsaron farin kaya ta NSCDC ne suka kama su kana suka mikasu ga hukumar NDLEA domin fadada bincike da gurfanar da su.

A karshe dai an gurfanar da su a kotu kan kara mai lamba FHC/L/292C/2021.

Da yake yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai Shari’a Akintayo Aluko na babban kotun tarayya da ke Legas ya kama tare da daure ‘yan Ghana din bisa safaran Wiwi inda ya daure kowannesu shekara takwas a gidan yari.

Wadanda aka dauren su ne: Victor Wuddah; Freeman Gazul; Adotete Joseph; Sottie Moses; Sottie Stephen; Christian Tette; Kanu Okonipa; Daniel Koyepti; da Kanu Natte.

NDLEA
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Na Ga Jiya Na Ga Yau, Babu Mai Tsorata Ni Kan Aikina Na Tace Fina-finai —Afakallah

Na Ga Jiya Na Ga Yau, Babu Mai Tsorata Ni Kan Aikina Na Tace Fina-finai —Afakallah

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.