• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Cafke Wani Basaraken Kauye Da Wasu Kan Safarar Miyagun Kwayoyi

by CMG Hausa
3 years ago
in Labarai
0
NDLEA Ta Cafke Wani Basaraken Kauye Da Wasu Kan Safarar Miyagun Kwayoyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) ta samu nasarar cafke hakimin kauyen Gidan Abba da ke karamar hukumar Bodinga a jihar Sokoto, Abubakar Ibrahim, bisa zarginsa da shiga hada-hadar miyagun kwayoyi.

Kakakin NDLEA, Femi Babafemi, ya ce, Basaraken na daga cikin mutum goma sha daya da aka kama bisa zargin hada-hadar kwaya 991,320 na maganin opioids da kuma Wiwi mai nauyin kilograms 1,251 da kuma Khat hadi da kilograms 46.637 na Methamphetamin, Cocaine da Heroin wadanda hukumar ta kamo a jihohi shida.

  • NDLEA Ta Cafke Mutum 192 Kan Safarar Miyagun Kwayoyi A Ebonyi

A ranar Laraba 26 ga watan Oktoba a filin sauka da tashi na Jirgin saman Murtala Muhammad da ke Ikeja Legas, jami’an NDLEA masu kula da hidimar shigo da kayayyaki da ke aiki a SAHCO sun kama katan guda 15 dauke da Kwayoyin tramadol 802,000 da aka shigo da su daga kasashen Dubai, UAE da kuma Karachi, Pakistan.

Dukka a wannan ranar, jami’an sun kuma cafke gwangwanin tumatur da aka shirya kaiwa Ingila.

Hukumar ta ce, bisa zurfafa bincike sun gano cewa gwangwanin Tumatur din an yi amfani da su wajen boye kwalayen tabar Wiwi 36 masu nauyin kilogirams 21.30 kuma jami’in dakon kayan mai suna Sodehinde Akinwale shi ma an kama shi tare da kayan.

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Kwanaki biyu bayan nan, jami’an hukumar da ke aiki tare da NAHCO masu kula da shigo da kaya a filin Jirgin Legas suka cafke katan biyar na busasshen Khat mai nauyin kilograms 107.70 da suka taho daga Bangkok da ke Thailand ta Dubai a Jirgin Emirates.

Kazalika, jami’an hukumar sun cafke wani matashi mai shekara 27 Madu Chukwuemeka Miracle a filin Jirgin saman kasa da kasa ta Akanu Ibiam, AIIA, Enugu bayan dawowarsa daga Nairobi, Kenya ta Addis Ababa, Ethiopia a ranar Laraba 26 ga watan Oktoba.

Da aka bincike kayansa an kama shi da kodin da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Shirya Taron Yada Ruhin Taron Wakilan JKS Karo Na 20 A Zanzibar

Next Post

Xi Ya Jaddada Sake Farfado Da Yankunan Karkara Yayin Da Ya Ziyarci Shaanxi Da Henan

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

56 minutes ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

3 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

4 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

5 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

8 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

9 hours ago
Next Post
Xi Ya Jaddada Sake Farfado Da Yankunan Karkara Yayin Da Ya Ziyarci Shaanxi Da Henan

Xi Ya Jaddada Sake Farfado Da Yankunan Karkara Yayin Da Ya Ziyarci Shaanxi Da Henan

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.