• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kwankwaso Na Shan Matsin Lamba Kan Yi Wa Atiku Mubaya’a

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kwankwaso

A daidai lokacin da ake kara kusantar babban zaben 2023, a ranar Asabar wata majiyarmu ta nakalto cewa wasu shugabannin Arewa sun fara yunkurin ganin an samu daidaito wajen tsayar da dan takarar shugaban kasa guda daya tilo daga yanki.

Majiyar ta shaida cewar shugabannin da dama a Arewa suna fatan cewa, Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP da ya zama dan takarar shugaban kasa daya tilau da zai fito a dama da shi a zaben 2023.

  • Gwamnan Bauchi Ya Amince Da Fitar Da Miliyan 500 Don Biyan Giratuti
  • Mutane 11 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Kogi

Hakan kai tsaye na kara fito da yadda ake yi wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso matsin lamba da ya amince ya mara wa Atiku baya domin yankin ta zama tana da dan takara guda.

“Mutanenmu sun cimma matsayar fitar da dan takara guda a zaben 2023 kuma tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar aka zaba na jam’iyyar PDP,” a cewar majiya da ta bukaci a sakaya sunanta.

A cewar majiyar hakan zai taimaka sosai wajen ganin Arewa ta samu nasarar lashe zaben shugaban kasa na 2023 da ke tafe, inda suka ce sun yi amannar muddin Atiku da Kwankwaso suka hada kai yankin zai iya lashen zaben.

LABARAI MASU NASABA

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

Majiyar wadda wani fitacce ne cikin kungiyar dattawan Arewa ya kara da cewa jigogi da daman gaske daga Arewa na kara matsa lamba wa dan takarar NNPP, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso da ya janye ya kuma mara wa Atiku baya.

“Ina mai tabbatar maka cewa shugabanninmu a Arewa suna kan matsa lamba wa Kwankwaso da ya janye neman takararsa ga Atiku domin cigaban jama’anmu da yankinmu,” a cewar majiyar.

Sai dai kuma duk da hakan, tawagar Kwankwaso dai sun nuna cewa tsohon gwamnan na jihar Kano ya yi biris da wannan matsin lambar da ake masa inda ya kara azama da burin cimma manufar da ya sanya a gaba.

Sai dai kuma karashin amincewar Kwankwaso na ya amince da wannan kokarin Bai rasa nasaba da dalilan da suka sanya shi fita daga cikin jam’iyyar PDP a baya.

“Zai yi matukar wahala Madugu ya mara wa PDP baya bisa yadda wasu makusantan Atiku ke bi da shi lokacin da yake tare da su, gaskiya dai da kamar wuya.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
Manyan Labarai

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025
Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
Manyan Labarai

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Manyan Labarai

NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa

October 31, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Bai Wa NYSC Tabbacin Samar Musu Da Tsaro A Zamfara 

‘Yansanda Sun Bai Wa NYSC Tabbacin Samar Musu Da Tsaro A Zamfara 

LABARAI MASU NASABA

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025
Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

October 31, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

October 31, 2025
Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

October 31, 2025
Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa

October 31, 2025

Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda

October 31, 2025
Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi

Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.