• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta kira ɓangarorin jami’an tsaro zuwa taron gaggawa domin tattauna hanyoyin hana ci gaba da cinna wa ofisoshin hukumar zaɓe wuta.

Taron wanda Kakakin Yaɗa Labarai na INEC, Festus Okoye ya sanar cewa ya gudana a ranar Juma’a, an tattauna matsalar hare-haren da aka kai ne sau biyu a cikin kwanaki biyu jere a jihohin Ogun da Osun.

  • Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

Okoye ya ce an gayyaci dukkan ɓangarorin da ke cikin Kwamitin Kula da Harkokin Tsaron Zaɓe (ICCES) domin tattauna matsalar, ganin yadda ranakun fara zaɓen sai kusantowa su ke yi.

“Mun samu labarin hare-haren banka wa ofisoshin INEC wuta har wurare biyu a jihohin Ogun da Osun. Wannan abu kuwa abin damuwa ne matuƙa.

INEC

Labarai Masu Nasaba

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

“Kwamishinan Zaɓe na Jihar Ogun, Niyi Ijalaiye ya sanar da cewa an kai wa ofishin INEC da ke Ƙaramar Hukumar Abeokuta ta Kudu harin da aka banka masa wuta.

“Maharan sun cimma mummunan burin su bayan sun fi ƙarfin jami’an tsaron da ke wurin, inda su ka banka wa ginin wuta.

“Daga cikin kayayyakin da aka yi asara akwai akwatin zaɓe 904, rumfar shiga a yi zaɓe 29, jakunkunan zuba kayan zaɓe 57, janareto takwas da kuma katin shaidar rajistar zaɓe 65,699 na waɗanda ba su kai ga karɓar na su ba,” inji Okoye.

Haka kuma ya ƙara da cewa an yi irin wannan harin banka wa ofishin INEC wuta a ranar Alhamis, “a Karamar Hukumar Ede ta Kudu, cikin Jihar Osun, kamar yadda Kwamishinan Zaɓe na Jihar, Mutiu Agboke ya sanar.”

Sai dai ya ce a nan ɓarnar ba ta yi muni ba kamar ta Jihar Ogun. Kuma ya ce a wannan ba a ƙone muhimman takardu da katin shaidar rajistar zaɓe, kamar yadda aka yi a Ogun ba.

Yayin da ake saura kwanaki 106 a fara zaɓe, Okoye ya ce tuni INEC ta fara aikawa da kayan zaɓe a ofisoshin ta jihohi daban-daban a ƙasar nan. Dalilin haka ne ya bayyana cewa hare-haren da aka fara kaiwa har ana banka wa ofishin da ake ajiyar kayan zaɓe wuta, abin damuwa ne kuma abin takaici.

Rahotanni da dama sun bayyana yadda aka yi amfani da sunƙin biredi aka babbake ofishin INEC a Ogun.

Kwana ɗaya kuma bayan harin Ogun, wasu taƙadarai sun banka wa ofishin INEC wuta a jihar Osun.

INEC

Wasu cikakkun ‘yan ta-kife sun bi daren Laraba, kafin wayewar garin Alhamis, su ka banka wa ofishin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) wuta, a Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun.

Ofishin da aka banka wa wutar ya na kusa da Iyaka ‘Mortuary’, cikin Ƙaramar Hukumar Abeokuta ta Kudu. ‘Yan ta-kifen da su ka banka masa wuta sun riƙa jiƙa sunƙin biredi cikin fetur, su na wurgawa a ofishin, sannan su ka ƙyasta wuta su ka tsere.

Mai gadin ofishin mai suna Azeez Hamzat, ya shaida cewa bayan an banka wutar, ya yi gaggawar kiran ‘yan sanda.

Majiya ta tabbatar cewa wasu kayayyaki da dama sun ƙone ƙurmus kafin jami’an kashe gobara su kai ɗauki.

Wakilin mu ya gano daga cikin ofisoshin da su ka ƙone, akwai ɗakin ajiyar kayayyaki, Ɗakin Yin Rajista, Zauren Shirya Taruka da sauran wasu wurare.

Kwamishinan Zaɓe na Jihar Ogun, Niyi Iyalaye ya tabbatar wa wakilin mu da wannan lamari da ya ce abin mamaki da takaici ne matuƙa.

“Amma dai yanzu mun kai rahoto wurin ‘yan sanda, kuma su na bincike,” inji shi.

Kakakin ‘Yan Sandan Jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi ya ce bai san da labarin ba, saboda bai ƙarasa ofis ba tukunna. Amma idan ya ƙarasa ya natsu, zai yi ƙarin bayani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dinkin Duniya Ta Koka Kan Rashin Tallafa Wa Mata Manoma A Nijeriya

Next Post

Firaministan Sin Ya Gana Da Shugabar Asusun IMF

Related

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
Labarai

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

11 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

12 hours ago
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

14 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

15 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

15 hours ago
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

18 hours ago
Next Post
Firaministan Sin Ya Gana Da Shugabar Asusun IMF

Firaministan Sin Ya Gana Da Shugabar Asusun IMF

LABARAI MASU NASABA

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.