ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dinkin Duniya Ta Koka Kan Rashin Tallafa Wa Mata Manoma A Nijeriya

by Sulaiman and Abubakar Abba
4 years ago
Duniya

Mataimakin wakiliyar mata a Majalisar dinkin duniya, Lansana Wonneh ya koka kan yadda mata manoma da ke a karkara a kasar nan, ba samun tallafin a kan Sana’ar ta su ta yin noma.

Ya sanar da cewa, matan manoma a karkara, na bayar da gagarumar gudunmawa,musamman wajen kara bunkasa samar da abinci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasar nan.

  • Ambaliyar Ruwa: Manoma Sun Samu Tallafin Asusun Bunkasa Noma

Ya sanar da hakan ne a wani taro a garin Kalaba a kan bikin zagayowar ranar mata manoma da ke a karkara ta duniya, inda ya ci gaba da cewa, an shirya taron ne domin a kara wa matan manoma karkashin kokarin da suke yi na samar da wadataccen abinci, musamman mai gina jiki a daukacin fadin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Wonneh ya ce an shirya taron ne domin zaburar da mata mazauna karkarar da ke kokarin samarwa, da sarrafawa, hadi da tattata abinci don ciyar da al’umma, duk da watsi da su da ake yi a kasar.
Ya ce Majalisar Dinkin Duniya za ta hada kai da Gwamnatin Nijeriya domin kawo gyara a lamarin.

“An shirya taron ne domin a kara wa matan manoma karkashin kokarin da suke yi na samar da wadataccen abinci, musamman mai gina jiki a daukacin fadin Nijeriya da kumakara karfafa masu gwiwa don su kara samar wa da kawunan su da kudaden shiga don sana’ar ta su ta kara bunkasa”.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

A cewar Wonneh ya zama wajibi matan manoman da ke a karkara a dinga tallafa mUsu, musamman idan aka yi dubi da irin wahalhalun da suke fuskanta a lokacin gudanar da aikin na su na noman.

Ya sanar da cewa, burin da majalisar ta ke da shi a kan matan manoman na karkara shine, aga suna samun kayan aikin noman, musamman na zamani da kuma samar masu da wadatattun kudade.

Ya yi nuni da cewa, tallafin zai taimaka masu matuka wajen kara mayar da hankali a kan gudanar da aikin na su na noman.
A wata sabuwa kuwa, an ankarar da gwamatin tarayya kan mahimmancin da ke tattare da san ya mata manoma a daukacin fadin kasar nan a cikin shirye-shiyen aikin noma na kasar.

Wannan ankararwar ta fito ne daga bakin Hajiya Amina Jibrin ita ce, shugabar kungiyar mata manoma kanana da da ke a kasar nan.
A Jawabin da ta yi a kwanan baya a bikin ranar abinci ta duniya Hajiya Amina Jibrin ta bukaci da a tallafa wa manoman, musamman idana aka yi dubi da yadda iftila’in ambaliyar ruwan sama ta yiwa wasu manoman kasar nan barna a gonakansu, inda ta sanar da cewa, matan manoma musamman na bukatar tallafi domin su samu samar ci gaba da yin noman da kuma tsyawa da kafafunsu.

Shugabar ta ci gaba da cewa, ya zama wajibi mahukunta a kasar nan da su samar da dokokin da za su bayar da damar tallafa wa kananan manoma, musamman a dora su a kan yin inshorar aikin noma.

Hajiya Amina ta kuma shawarci gwamnatin jihar Bauchi ta kebe kanana manoman da ke a fadin jihar, bisa yarjejeniyar da aka sa wa hannu ta Maputo.

Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Duniya
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.