• English
  • Business News
Tuesday, June 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Kasashen Yamma Su Nuna Sahihanci

by Sulaiman
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Kasashen Yamma Su Nuna Sahihanci

FILE - People transport cassava in a canoes along flooded residential streets after a heavy downpour In Bayelsa, Nigeria, Oct. 20, 2022. West and Central African countries are battling deadly floods that have upended lives and livelihoods, raising fears of further disruption of food supplies in many areas battling armed conflict. “Above-average rainfall and devastating flooding” have affected 5 million people this year in 19 countries across West and Central Africa, according to a new U.N. World Food Program situation report. (AP Photo/Reed Joshua, File)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, ko kun karanta bayanin da shugaba Muhammadu Buhari ya rubuta a gefen taron sauyin yanayi na COP27, wanda aka buga shi kan shafin yanar gizo na jaridar Washington Post ta kasar Amurka?

Na karanta bayanin, kuma na ji yadda shugaban ya nuna rashin gamsuwa, da takaici, inda ya soki kasashen yamma bisa rashin sauke nauyinsu.

  • Ya Kamata Amurka Ta Hada Gwiwa Da Sin Don Mayar Da Huldar Dake Tsakaninsu Kan Hanyar Da Ta Dace

A cewar shugaban, ko da yake kasashen yamma sun yi alkawarin samar da tallafi na dala biliyan 100 ga kasashe masu tasowa a kowace shekara, don taimaka musu wajen tinkarar batun sauyawar yanayi, amma ba su taba cika alkawarin ba.

Har ila yau, a wajen taron COP27, an nanata bukatar biyan diyya ga kasashe masu tasowa, bisa hasarar da suka samu sakamakon sauyin yanayin duniya, amma duk da haka kasashen yamma sun yi shiru.

Na fahimci maganar shugaba Buhari da fushinsa, saboda nahiyar Afirka tana shan wahalar matsalolin sauyin yanayi sosai, ko da yake iska mai dumama yanayin da nahiyar ke fitarwa ba ta da yawa.

Labarai Masu Nasaba

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

A daura da haka, kasashen yamma su ne suka fi samar da iska mai gurbata muhalli cikin shekaru kimanin 200 da suka gabata, kana zuwa yanzu sun fi samun kudi da fasahohi da za su iya amfanar kasashe masu tasowa. Amma duk da haka ba su son sauke nauyin dake bisa wuyansu.

Sa’an nan rashin sauke nauyin na kasashen yamma, bai tsaya kan tsumulmularsu ba, har ma ya shafi wadannan fannoni:
Da farko, manufar da kasashen yamma suka gabatar ta rage fitar da iskar dumama yanayi, ba ta dace da yanayin da kasashen Afirka suke ciki ba.

Saboda nahiyar Afirka ta riga ta kasance yankin da ke fitar da mafi kankantar iskar Carbon. Abun da kasashen Afirka suke bukata shi ne karfafa kwarewarsu a fannin tinkarar bala’u, da kula da jama’ar da iftila’u suka ritsa da su, maimakon daidiata tsarin makamashi ba tare da lura da matsi a fannin tattalin arziki ba.

Na biyu, shi ne kasashen yamma na neman yin amfani da batun sauyawar yanayi wajen kare moriyarsu, har da a nahiyar Afirka. Misali, manufar karbar karin harajin kwastam kan kayayyakin da suke cewa wai ba irin na kare muhalli ba ne da kungiyar kasashen Turai ta EU ta fara aiwatarwa a bara, tana haifar da karin kudin shiga har Euro biliyan 5 zuwa 14 ga kungiyar EU a duk shekara, duk da cewa manufar ba ta dace da gatan da wasu kasashen Afirka suka samu, a fannin fitar da kayayyakinsu zuwa kasuwannin nahiyar Turai ba.

Hakika, bisa karfin tattalin arzikin kasashen yamma, da ingancin fasahohinsu, za su iya taimakawa kasashen Afirka a fannoni daban daban. Idan har mun dauki hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka ta fuskar tinkarar batun sauyin yanayi a matsayin misali: Kasar Sin tana raba bayanan taurarin dan Adam tare da kasashen dake kudancin nahiyar Afirka, da ba da tallafin nau’rorin binciken yanayi masu sarrafa kansu ga kasashen Comoros, da Kenya, da taimakawa kasashen dake yankin Sahel, irinsu Niger da Burkina faso, wajen dasa itatuwa na kare iska, da dai sauransu. Ban da haka, fasahar noman sabon nau’in shinkafa da kasar Sin ta koyar a kasashen Najeriya, da Madagascar, da dai sauransu, ta sa ana samun damar tabbatar da samun isashen abinci, yayin da ake fama da bala’i.

Haka zalika, kamfanonin kasar Sin sun gina tashoshin samar da wutar lantarki ta yin amfani da zafin rana da karfin iska, a kasashen Kenya da Afirka ta Kudu, wadanda suke ba da taimako ga al’ummun kasashen, a kokarinsu na kyautata zaman rayuwa, da kare muhallin halittu.

Ta hanyar kwatanta hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin, za mu iya gane cewa, kasashen yamma ba su nuna sahihanci sosai ba.

Kullum suna neman jagorantar aikin tinkarar sauyawar yanayi na duniya, amma sakamakon da suke samarwa ba shi da yawa, sakamakon yadda suke tsumulmular raba moriya ga kasashe masu tasowa.

A gani na, ya kamata kasashen yamma su kara nuna sahihanci, da daukar karin takamaiman matakai na taimakawa kasashen Afirka, saboda hakan ne kadai zai dace da matsayinsu na kasashe masu sukuni. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Air Peace Ya Dakatar Da Zirga-Zirgar Jiragen Sama Zuwa Dubai Saboda Haramcin Biza

Next Post

Nan Kusa Rikicin Atiku Da Gwamnonin PDP ‘Yan G5 Zai Zama Tarihi – Saraki

Related

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu
Daga Birnin Sin

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

12 hours ago
Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda
Daga Birnin Sin

Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

12 hours ago
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu
Daga Birnin Sin

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

13 hours ago
Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

14 hours ago
Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev

15 hours ago
Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Wanzar Da Bunkasar Masana’antu A Nahiyar Afirka, In Ji Wani Masanin Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Wanzar Da Bunkasar Masana’antu A Nahiyar Afirka, In Ji Wani Masanin Tattalin Arziki

15 hours ago
Next Post
Nan Kusa Rikicin Atiku Da Gwamnonin PDP ‘Yan G5 Zai Zama Tarihi – Saraki

Nan Kusa Rikicin Atiku Da Gwamnonin PDP 'Yan G5 Zai Zama Tarihi - Saraki

LABARAI MASU NASABA

Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

June 17, 2025
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

June 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

June 17, 2025
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

June 16, 2025
Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

June 16, 2025
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

June 16, 2025
Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake

Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake

June 16, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev

Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev

June 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.