ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Kasashen Yamma Su Nuna Sahihanci

by Sulaiman
4 years ago
FILE - People transport cassava in a canoes along flooded residential streets after a heavy downpour In Bayelsa, Nigeria, Oct. 20, 2022. West and Central African countries are battling deadly floods that have upended lives and livelihoods, raising fears of further disruption of food supplies in many areas battling armed conflict. “Above-average rainfall and devastating flooding” have affected 5 million people this year in 19 countries across West and Central Africa, according to a new U.N. World Food Program situation report. (AP Photo/Reed Joshua, File)

FILE - People transport cassava in a canoes along flooded residential streets after a heavy downpour In Bayelsa, Nigeria, Oct. 20, 2022. West and Central African countries are battling deadly floods that have upended lives and livelihoods, raising fears of further disruption of food supplies in many areas battling armed conflict. “Above-average rainfall and devastating flooding” have affected 5 million people this year in 19 countries across West and Central Africa, according to a new U.N. World Food Program situation report. (AP Photo/Reed Joshua, File)

Abokaina, ko kun karanta bayanin da shugaba Muhammadu Buhari ya rubuta a gefen taron sauyin yanayi na COP27, wanda aka buga shi kan shafin yanar gizo na jaridar Washington Post ta kasar Amurka?

Na karanta bayanin, kuma na ji yadda shugaban ya nuna rashin gamsuwa, da takaici, inda ya soki kasashen yamma bisa rashin sauke nauyinsu.

  • Ya Kamata Amurka Ta Hada Gwiwa Da Sin Don Mayar Da Huldar Dake Tsakaninsu Kan Hanyar Da Ta Dace

A cewar shugaban, ko da yake kasashen yamma sun yi alkawarin samar da tallafi na dala biliyan 100 ga kasashe masu tasowa a kowace shekara, don taimaka musu wajen tinkarar batun sauyawar yanayi, amma ba su taba cika alkawarin ba.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, a wajen taron COP27, an nanata bukatar biyan diyya ga kasashe masu tasowa, bisa hasarar da suka samu sakamakon sauyin yanayin duniya, amma duk da haka kasashen yamma sun yi shiru.

Na fahimci maganar shugaba Buhari da fushinsa, saboda nahiyar Afirka tana shan wahalar matsalolin sauyin yanayi sosai, ko da yake iska mai dumama yanayin da nahiyar ke fitarwa ba ta da yawa.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

A daura da haka, kasashen yamma su ne suka fi samar da iska mai gurbata muhalli cikin shekaru kimanin 200 da suka gabata, kana zuwa yanzu sun fi samun kudi da fasahohi da za su iya amfanar kasashe masu tasowa. Amma duk da haka ba su son sauke nauyin dake bisa wuyansu.

Sa’an nan rashin sauke nauyin na kasashen yamma, bai tsaya kan tsumulmularsu ba, har ma ya shafi wadannan fannoni:
Da farko, manufar da kasashen yamma suka gabatar ta rage fitar da iskar dumama yanayi, ba ta dace da yanayin da kasashen Afirka suke ciki ba.

Saboda nahiyar Afirka ta riga ta kasance yankin da ke fitar da mafi kankantar iskar Carbon. Abun da kasashen Afirka suke bukata shi ne karfafa kwarewarsu a fannin tinkarar bala’u, da kula da jama’ar da iftila’u suka ritsa da su, maimakon daidiata tsarin makamashi ba tare da lura da matsi a fannin tattalin arziki ba.

Na biyu, shi ne kasashen yamma na neman yin amfani da batun sauyawar yanayi wajen kare moriyarsu, har da a nahiyar Afirka. Misali, manufar karbar karin harajin kwastam kan kayayyakin da suke cewa wai ba irin na kare muhalli ba ne da kungiyar kasashen Turai ta EU ta fara aiwatarwa a bara, tana haifar da karin kudin shiga har Euro biliyan 5 zuwa 14 ga kungiyar EU a duk shekara, duk da cewa manufar ba ta dace da gatan da wasu kasashen Afirka suka samu, a fannin fitar da kayayyakinsu zuwa kasuwannin nahiyar Turai ba.

Hakika, bisa karfin tattalin arzikin kasashen yamma, da ingancin fasahohinsu, za su iya taimakawa kasashen Afirka a fannoni daban daban. Idan har mun dauki hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka ta fuskar tinkarar batun sauyin yanayi a matsayin misali: Kasar Sin tana raba bayanan taurarin dan Adam tare da kasashen dake kudancin nahiyar Afirka, da ba da tallafin nau’rorin binciken yanayi masu sarrafa kansu ga kasashen Comoros, da Kenya, da taimakawa kasashen dake yankin Sahel, irinsu Niger da Burkina faso, wajen dasa itatuwa na kare iska, da dai sauransu. Ban da haka, fasahar noman sabon nau’in shinkafa da kasar Sin ta koyar a kasashen Najeriya, da Madagascar, da dai sauransu, ta sa ana samun damar tabbatar da samun isashen abinci, yayin da ake fama da bala’i.

Haka zalika, kamfanonin kasar Sin sun gina tashoshin samar da wutar lantarki ta yin amfani da zafin rana da karfin iska, a kasashen Kenya da Afirka ta Kudu, wadanda suke ba da taimako ga al’ummun kasashen, a kokarinsu na kyautata zaman rayuwa, da kare muhallin halittu.

Ta hanyar kwatanta hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin, za mu iya gane cewa, kasashen yamma ba su nuna sahihanci sosai ba.

Kullum suna neman jagorantar aikin tinkarar sauyawar yanayi na duniya, amma sakamakon da suke samarwa ba shi da yawa, sakamakon yadda suke tsumulmular raba moriya ga kasashe masu tasowa.

A gani na, ya kamata kasashen yamma su kara nuna sahihanci, da daukar karin takamaiman matakai na taimakawa kasashen Afirka, saboda hakan ne kadai zai dace da matsayinsu na kasashe masu sukuni. (Bello Wang)

Kasashen yamma
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Nan Kusa Rikicin Atiku Da Gwamnonin PDP ‘Yan G5 Zai Zama Tarihi – Saraki

Nan Kusa Rikicin Atiku Da Gwamnonin PDP 'Yan G5 Zai Zama Tarihi - Saraki

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.