ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Kasashen Yamma Su Nuna Sahihanci

by Sulaiman
4 years ago
FILE - People transport cassava in a canoes along flooded residential streets after a heavy downpour In Bayelsa, Nigeria, Oct. 20, 2022. West and Central African countries are battling deadly floods that have upended lives and livelihoods, raising fears of further disruption of food supplies in many areas battling armed conflict. “Above-average rainfall and devastating flooding” have affected 5 million people this year in 19 countries across West and Central Africa, according to a new U.N. World Food Program situation report. (AP Photo/Reed Joshua, File)

FILE - People transport cassava in a canoes along flooded residential streets after a heavy downpour In Bayelsa, Nigeria, Oct. 20, 2022. West and Central African countries are battling deadly floods that have upended lives and livelihoods, raising fears of further disruption of food supplies in many areas battling armed conflict. “Above-average rainfall and devastating flooding” have affected 5 million people this year in 19 countries across West and Central Africa, according to a new U.N. World Food Program situation report. (AP Photo/Reed Joshua, File)

Abokaina, ko kun karanta bayanin da shugaba Muhammadu Buhari ya rubuta a gefen taron sauyin yanayi na COP27, wanda aka buga shi kan shafin yanar gizo na jaridar Washington Post ta kasar Amurka?

Na karanta bayanin, kuma na ji yadda shugaban ya nuna rashin gamsuwa, da takaici, inda ya soki kasashen yamma bisa rashin sauke nauyinsu.

  • Ya Kamata Amurka Ta Hada Gwiwa Da Sin Don Mayar Da Huldar Dake Tsakaninsu Kan Hanyar Da Ta Dace

A cewar shugaban, ko da yake kasashen yamma sun yi alkawarin samar da tallafi na dala biliyan 100 ga kasashe masu tasowa a kowace shekara, don taimaka musu wajen tinkarar batun sauyawar yanayi, amma ba su taba cika alkawarin ba.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, a wajen taron COP27, an nanata bukatar biyan diyya ga kasashe masu tasowa, bisa hasarar da suka samu sakamakon sauyin yanayin duniya, amma duk da haka kasashen yamma sun yi shiru.

Na fahimci maganar shugaba Buhari da fushinsa, saboda nahiyar Afirka tana shan wahalar matsalolin sauyin yanayi sosai, ko da yake iska mai dumama yanayin da nahiyar ke fitarwa ba ta da yawa.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A daura da haka, kasashen yamma su ne suka fi samar da iska mai gurbata muhalli cikin shekaru kimanin 200 da suka gabata, kana zuwa yanzu sun fi samun kudi da fasahohi da za su iya amfanar kasashe masu tasowa. Amma duk da haka ba su son sauke nauyin dake bisa wuyansu.

Sa’an nan rashin sauke nauyin na kasashen yamma, bai tsaya kan tsumulmularsu ba, har ma ya shafi wadannan fannoni:
Da farko, manufar da kasashen yamma suka gabatar ta rage fitar da iskar dumama yanayi, ba ta dace da yanayin da kasashen Afirka suke ciki ba.

Saboda nahiyar Afirka ta riga ta kasance yankin da ke fitar da mafi kankantar iskar Carbon. Abun da kasashen Afirka suke bukata shi ne karfafa kwarewarsu a fannin tinkarar bala’u, da kula da jama’ar da iftila’u suka ritsa da su, maimakon daidiata tsarin makamashi ba tare da lura da matsi a fannin tattalin arziki ba.

Na biyu, shi ne kasashen yamma na neman yin amfani da batun sauyawar yanayi wajen kare moriyarsu, har da a nahiyar Afirka. Misali, manufar karbar karin harajin kwastam kan kayayyakin da suke cewa wai ba irin na kare muhalli ba ne da kungiyar kasashen Turai ta EU ta fara aiwatarwa a bara, tana haifar da karin kudin shiga har Euro biliyan 5 zuwa 14 ga kungiyar EU a duk shekara, duk da cewa manufar ba ta dace da gatan da wasu kasashen Afirka suka samu, a fannin fitar da kayayyakinsu zuwa kasuwannin nahiyar Turai ba.

Hakika, bisa karfin tattalin arzikin kasashen yamma, da ingancin fasahohinsu, za su iya taimakawa kasashen Afirka a fannoni daban daban. Idan har mun dauki hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka ta fuskar tinkarar batun sauyin yanayi a matsayin misali: Kasar Sin tana raba bayanan taurarin dan Adam tare da kasashen dake kudancin nahiyar Afirka, da ba da tallafin nau’rorin binciken yanayi masu sarrafa kansu ga kasashen Comoros, da Kenya, da taimakawa kasashen dake yankin Sahel, irinsu Niger da Burkina faso, wajen dasa itatuwa na kare iska, da dai sauransu. Ban da haka, fasahar noman sabon nau’in shinkafa da kasar Sin ta koyar a kasashen Najeriya, da Madagascar, da dai sauransu, ta sa ana samun damar tabbatar da samun isashen abinci, yayin da ake fama da bala’i.

Haka zalika, kamfanonin kasar Sin sun gina tashoshin samar da wutar lantarki ta yin amfani da zafin rana da karfin iska, a kasashen Kenya da Afirka ta Kudu, wadanda suke ba da taimako ga al’ummun kasashen, a kokarinsu na kyautata zaman rayuwa, da kare muhallin halittu.

Ta hanyar kwatanta hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin, za mu iya gane cewa, kasashen yamma ba su nuna sahihanci sosai ba.

Kullum suna neman jagorantar aikin tinkarar sauyawar yanayi na duniya, amma sakamakon da suke samarwa ba shi da yawa, sakamakon yadda suke tsumulmular raba moriya ga kasashe masu tasowa.

A gani na, ya kamata kasashen yamma su kara nuna sahihanci, da daukar karin takamaiman matakai na taimakawa kasashen Afirka, saboda hakan ne kadai zai dace da matsayinsu na kasashe masu sukuni. (Bello Wang)

Kasashen yamma
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Nan Kusa Rikicin Atiku Da Gwamnonin PDP ‘Yan G5 Zai Zama Tarihi – Saraki

Nan Kusa Rikicin Atiku Da Gwamnonin PDP 'Yan G5 Zai Zama Tarihi - Saraki

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.