• English
  • Business News
Sunday, May 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marwa Ya Kara Samun Lambar Yabo

by Leadership Hausa
3 years ago
in Labarai
0
Marwa Ya Kara Samun Lambar Yabo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A karo na biyar a cikin watanni biyu, shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA), Burgediya Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya) ya samu karin lambar yabo.

Idan ba a manta ba dai a watan da ta gabata, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karrama Marwa sau biyu, inda ya ba shi lambar yabo ta kasa matakin CON, kazalika, kuma ya kara karrama shi bayan mako guda da lambar yabo bisa bajintar da ya nuna a yaki da miyagun kwayoyi.

  • Buhari Ya Taya Jonathan Murnar Cika Shekaru 65 
  • Adabin Zamanin Da Na Sin (3) Wakokin Daular Tang

Biyo bayan wadannan karramawar ne, kungiyar al’umman garin Michika na Jihar Adamawa suka yi taro na musamman, inda suka karrama Marwa a matsayin dansu da ya nuna bajinta na musamman a Nijeriya. Kungiyar ta karrama shi ne tare da wasu fitattun ‘yan garin na Michika.

Babu shakka bajintar Marwa na inganta yaki da ta’amuli da miyagun kwayoyi abu ne da ya bayyana, lura da nasarori da hukumar NDLEA take samu a kullum. Ko a yau, hukumar ta fitar da sanarwar kama sama da tan bakwai na wiwi wanda yawan sa ya haura kilogiram dubu bakawai.

Alkaluman bayanai sun yi nuni da cewa, hukumar NDLEA ta kama sama da mutane 8,996 a cikin shekarar 2022. A bangaren kayan maye kuma, hukumar ta kama sama da kilogiram 219,576 na miyagun kwayoyi a wurare daban-daban a Nijeriya a cikin shekarar nan. Kazalika, hukumar ta lalata gonakin wiwi wanda yawan su ya kai hekta 324. Haka ma hukumar ta yi nasarar gyara tunanin (rehabilitation) na mashaya 6,244 a cikin shekarar nan.

Labarai Masu Nasaba

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

A kwanan nan ne hukumar ta yi shahararren kamun nan da ta yi na hodar iblis wanda yawansa ya kai tan 1.8 a wani gidan ajiya a Jihar Legas. Hodar iblis din wanda aka kiyasta kudinsa ya kai Naira biliyan 194, ya kasance kamu mafi girma na hodar iblis da hukumar ta yi a lokaci daya tun bayan kafa hukumar a shekaru 30 da suka wuce.

Adadin nasarorin da Marwa ya samu a yayin shugabancin hukumar NDLEA ba za su kirgu ba. Kuma wannan ba shi ne karshe ba, saboda har yanzu bakin alkalami a jike yake da tawadar rubuta nasarori da hukumar take ci gaba da samu a yaki da fataucin miyagun kwayoyi.

Idan akwai abun da Marwa ya nuna wa duniya da ya kamata na baya su yi koyi da shi, to ba zai wuce tsayuwa da gaske wajen aiwatar da aiki a duk inda ya samu kansa ba. Za a gane hakan idan aka waiwaya zuwa mukaman da ya rike a baya, kamar na gwamnan Jihar Legas da makamantansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GirmamawaLambar YaboMarwaNDLEA
ShareTweetSendShare
Previous Post

FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

Next Post

Shugaba Buhari Zai Kaddamar Da Aikin Tono Man Fetur A Jihohin Bauchi Da Gombe

Related

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake
Labarai

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

1 hour ago
Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota
Labarai

Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

2 hours ago
Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa
Labarai

Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

4 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Labarai

Tangarɗar Na’ura: JAMB Ta Sake Fitar Da Sakamakon Jarabawar UTME Ta 2025

6 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

Ya Kuɓuta A Hannun ‘Yan Bindiga Bayan Shafe Kwanaki 8 Yana Gudu A Dajin Sokoto Da Neja

6 hours ago
katsina
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 5 A Katsina

8 hours ago
Next Post
Shugaba Buhari Zai Kaddamar Da Aikin Tono Man Fetur A Jihohin Bauchi Da Gombe

Shugaba Buhari Zai Kaddamar Da Aikin Tono Man Fetur A Jihohin Bauchi Da Gombe

LABARAI MASU NASABA

Chelsea, Man City, Newcastle Sun Samu Gurbi A Gasar Zakarun Turai Ta Baɗi

Chelsea, Man City, Newcastle Sun Samu Gurbi A Gasar Zakarun Turai Ta Baɗi

May 25, 2025
Xi Jinping Ya Taya Murnar Bude Bikin Baje Kolin Kayayyaki Na Yammacin Sin

Xi Jinping Ya Taya Murnar Bude Bikin Baje Kolin Kayayyaki Na Yammacin Sin

May 25, 2025
Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

May 25, 2025
Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

May 25, 2025
Ruhin Yuan Longping Ya Ba Da Tabbaci Ga Samar Da Isashen Hatsi a Nahiyar Afirka

Ruhin Yuan Longping Ya Ba Da Tabbaci Ga Samar Da Isashen Hatsi a Nahiyar Afirka

May 25, 2025
Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu

Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu

May 25, 2025
Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

May 25, 2025
An Kaddamar Da Babban Filin Wasan Da Kasar Sin Ta Gina Wa Kasar Chadi Kyauta

An Kaddamar Da Babban Filin Wasan Da Kasar Sin Ta Gina Wa Kasar Chadi Kyauta

May 25, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

Tangarɗar Na’ura: JAMB Ta Sake Fitar Da Sakamakon Jarabawar UTME Ta 2025

May 25, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Ya Kuɓuta A Hannun ‘Yan Bindiga Bayan Shafe Kwanaki 8 Yana Gudu A Dajin Sokoto Da Neja

May 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.