• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marwa Ya Kara Samun Lambar Yabo

by Leadership Hausa
3 years ago
in Labarai
0
Marwa Ya Kara Samun Lambar Yabo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A karo na biyar a cikin watanni biyu, shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA), Burgediya Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya) ya samu karin lambar yabo.

Idan ba a manta ba dai a watan da ta gabata, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karrama Marwa sau biyu, inda ya ba shi lambar yabo ta kasa matakin CON, kazalika, kuma ya kara karrama shi bayan mako guda da lambar yabo bisa bajintar da ya nuna a yaki da miyagun kwayoyi.

  • Buhari Ya Taya Jonathan Murnar Cika Shekaru 65 
  • Adabin Zamanin Da Na Sin (3) Wakokin Daular Tang

Biyo bayan wadannan karramawar ne, kungiyar al’umman garin Michika na Jihar Adamawa suka yi taro na musamman, inda suka karrama Marwa a matsayin dansu da ya nuna bajinta na musamman a Nijeriya. Kungiyar ta karrama shi ne tare da wasu fitattun ‘yan garin na Michika.

Babu shakka bajintar Marwa na inganta yaki da ta’amuli da miyagun kwayoyi abu ne da ya bayyana, lura da nasarori da hukumar NDLEA take samu a kullum. Ko a yau, hukumar ta fitar da sanarwar kama sama da tan bakwai na wiwi wanda yawan sa ya haura kilogiram dubu bakawai.

Alkaluman bayanai sun yi nuni da cewa, hukumar NDLEA ta kama sama da mutane 8,996 a cikin shekarar 2022. A bangaren kayan maye kuma, hukumar ta kama sama da kilogiram 219,576 na miyagun kwayoyi a wurare daban-daban a Nijeriya a cikin shekarar nan. Kazalika, hukumar ta lalata gonakin wiwi wanda yawan su ya kai hekta 324. Haka ma hukumar ta yi nasarar gyara tunanin (rehabilitation) na mashaya 6,244 a cikin shekarar nan.

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

A kwanan nan ne hukumar ta yi shahararren kamun nan da ta yi na hodar iblis wanda yawansa ya kai tan 1.8 a wani gidan ajiya a Jihar Legas. Hodar iblis din wanda aka kiyasta kudinsa ya kai Naira biliyan 194, ya kasance kamu mafi girma na hodar iblis da hukumar ta yi a lokaci daya tun bayan kafa hukumar a shekaru 30 da suka wuce.

Adadin nasarorin da Marwa ya samu a yayin shugabancin hukumar NDLEA ba za su kirgu ba. Kuma wannan ba shi ne karshe ba, saboda har yanzu bakin alkalami a jike yake da tawadar rubuta nasarori da hukumar take ci gaba da samu a yaki da fataucin miyagun kwayoyi.

Idan akwai abun da Marwa ya nuna wa duniya da ya kamata na baya su yi koyi da shi, to ba zai wuce tsayuwa da gaske wajen aiwatar da aiki a duk inda ya samu kansa ba. Za a gane hakan idan aka waiwaya zuwa mukaman da ya rike a baya, kamar na gwamnan Jihar Legas da makamantansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GirmamawaLambar YaboMarwaNDLEA
ShareTweetSendShare
Previous Post

FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

Next Post

Shugaba Buhari Zai Kaddamar Da Aikin Tono Man Fetur A Jihohin Bauchi Da Gombe

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

3 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

5 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

5 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

7 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata

12 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

13 hours ago
Next Post
Shugaba Buhari Zai Kaddamar Da Aikin Tono Man Fetur A Jihohin Bauchi Da Gombe

Shugaba Buhari Zai Kaddamar Da Aikin Tono Man Fetur A Jihohin Bauchi Da Gombe

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.