ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marwa Ya Kara Samun Lambar Yabo

by Leadership Hausa
4 years ago
Marwa

A karo na biyar a cikin watanni biyu, shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA), Burgediya Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya) ya samu karin lambar yabo.

Idan ba a manta ba dai a watan da ta gabata, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karrama Marwa sau biyu, inda ya ba shi lambar yabo ta kasa matakin CON, kazalika, kuma ya kara karrama shi bayan mako guda da lambar yabo bisa bajintar da ya nuna a yaki da miyagun kwayoyi.

  • Buhari Ya Taya Jonathan Murnar Cika Shekaru 65 
  • Adabin Zamanin Da Na Sin (3) Wakokin Daular Tang

Biyo bayan wadannan karramawar ne, kungiyar al’umman garin Michika na Jihar Adamawa suka yi taro na musamman, inda suka karrama Marwa a matsayin dansu da ya nuna bajinta na musamman a Nijeriya. Kungiyar ta karrama shi ne tare da wasu fitattun ‘yan garin na Michika.

ADVERTISEMENT

Babu shakka bajintar Marwa na inganta yaki da ta’amuli da miyagun kwayoyi abu ne da ya bayyana, lura da nasarori da hukumar NDLEA take samu a kullum. Ko a yau, hukumar ta fitar da sanarwar kama sama da tan bakwai na wiwi wanda yawan sa ya haura kilogiram dubu bakawai.

Alkaluman bayanai sun yi nuni da cewa, hukumar NDLEA ta kama sama da mutane 8,996 a cikin shekarar 2022. A bangaren kayan maye kuma, hukumar ta kama sama da kilogiram 219,576 na miyagun kwayoyi a wurare daban-daban a Nijeriya a cikin shekarar nan. Kazalika, hukumar ta lalata gonakin wiwi wanda yawan su ya kai hekta 324. Haka ma hukumar ta yi nasarar gyara tunanin (rehabilitation) na mashaya 6,244 a cikin shekarar nan.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A kwanan nan ne hukumar ta yi shahararren kamun nan da ta yi na hodar iblis wanda yawansa ya kai tan 1.8 a wani gidan ajiya a Jihar Legas. Hodar iblis din wanda aka kiyasta kudinsa ya kai Naira biliyan 194, ya kasance kamu mafi girma na hodar iblis da hukumar ta yi a lokaci daya tun bayan kafa hukumar a shekaru 30 da suka wuce.

Adadin nasarorin da Marwa ya samu a yayin shugabancin hukumar NDLEA ba za su kirgu ba. Kuma wannan ba shi ne karshe ba, saboda har yanzu bakin alkalami a jike yake da tawadar rubuta nasarori da hukumar take ci gaba da samu a yaki da fataucin miyagun kwayoyi.

Idan akwai abun da Marwa ya nuna wa duniya da ya kamata na baya su yi koyi da shi, to ba zai wuce tsayuwa da gaske wajen aiwatar da aiki a duk inda ya samu kansa ba. Za a gane hakan idan aka waiwaya zuwa mukaman da ya rike a baya, kamar na gwamnan Jihar Legas da makamantansu.

Marwa
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Shugaba Buhari Zai Kaddamar Da Aikin Tono Man Fetur A Jihohin Bauchi Da Gombe

Shugaba Buhari Zai Kaddamar Da Aikin Tono Man Fetur A Jihohin Bauchi Da Gombe

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.