• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sulhu Da Atiku: Sabbin Sharruddan Da Fusatattun Gwamnonin PDP Suka Gindaya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sulhu Da Atiku: Sabbin Sharruddan Da Fusatattun Gwamnonin PDP Suka Gindaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadi da ta gabata, fusatattun gwamnonin PDP da ake kira da G-5 sun gindaya sababbin sharudda kafin su goyi bayan Atiku Abubakar.

Wannan yana zuwa ne a daidai lokacin da tawagar dan takarar shugaban kasa na APC, Bola Ahmed Tinubu da takwaransa na jam’iyyar LP, Peter Obi suke zawarcin gwamnoni domin su mara musu baya a zaben shugaban kasa na 2023.

  • Tsoma Baki Da Lalata Tsarin Samar Da Kayayyaki Da Amurka Ke Yi Bai Samu Karbuwa Ba
  • Dalibi Ya Rataye Kansa Har Lahira Saboda Budurwarsa Ta Auri Wani A Gombe

Da suke jawabi jin kadan bayan ganawar sirri a Jihar Legas, gwamnonin sun bayyana cewa har yanzu kofar yin silhu da Atiku a bude take.

A wurin ganawar akwai gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike da gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde da gwamnan Jihar Benuwai, Samuel Ortom da gwamnan Jihar Inugu, Ifeanyi Ugwuanyi da gwamnan Jihar Abiya, Okezie Ikpeazu da tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP, Cif Olabode George da tsofaffin gwamnoni wadanda suka hada da Ayodele Fayose (Ekiti) da Donald Duke (Kuros Riba) da Olusegun Mimiko (Ondo) da kuma Jonah Jang (Filato).

Haka kuma akwai tsohon ministan shari’a, Mohammed Adoke da mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na yankin kudu, Taofeek Arapaja da Sanata Nasif Suleiman da Sanata Sandy Onor da kuma Sanato Sam Ohabunwa.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Ganawar ta gudana kwanaki kadan bayan gwamnaoni sun bayyana dan takarar gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara. Sun gudanar da irin wannan ganawa a Inugu da Benuwai da kuma kasashen ketare. Gwamnonin sun yi bore ga Atiku kan kin dakatar da shugaban jam’iyyar PDP, Iyorchia Ayu.

Da yake magana a wurin ganawar, Makinde ya bayyana cewa shi da sauran abokanansa za su ci gaba da fafatuka har sai shugabannin jam’iyya da sauran dattawan jam’iyyar sun dawo daga hayyacinsu.

Ya ce, “Mun hadu ne a wannan wuri domin ganawa da sauran jiga-jigan jam’iyyar PDP. Mu ne gwamnonin guda biyar da ake kira G-5, wanda muka kasance sabuwar tawaga masu mutunci.

“Idan aka kallemu za a ga cewa gwamnoni ne guda biyar da suke ci gaba da fafatuka, kuma mu a yankin kudu maso yamma mun sake bibiyan al’amuran jam’iyyar domin ganin abubuwan da suke gudana game da zabe mai zuwa.”

Bayan ganawar sirrin, Jang ya jaddada cewa suna nan a kan matakansu kan abubuwan da suka tattauna a Fatakwal.

“Bayan nazari kan abubuwan da suke gudana a jam’iyyar, mun cimma matsaya kan yanke hukuncin da muka zantar a garin Fatakwal. Sannan mun gana a nan ne domin jaddada matsayarmu wajen bude kofar tattaunawa da jam’iyyarmu ta PDP,” in ji shi.

Gwamnonin sun gudanar da ganawar ce a dakin taro na George da ke Ikoyi, inda Wike ya bayyana cewa za su goyi bayan jam’iyyarsu a zabe mai zuwa matukar aka biya musu bukatocinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuG5PDPSharudaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

Next Post

Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.