ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
9 months ago
INEC

Sabon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan zai fuskanci wasu manyan kalubale a shugabancin hukumar, yayin da ya gada tsarin zabe da ke cike da cece-kuce, rashin amincewar masu jefa kuri’a, da matsin lamba na tabbatar da cewa an gudanar da zabe mai inganci.

 

An nada shi ne bayan amincewar majalisar zartarwa ta tarayya a lokacin zaman majalisar wanda ya gudana a Abuja ranar Alhamis da ta gabata. Ya dai kasance dan asalin Jihar Kogi ne da ke arewa ta tsakiya.

ADVERTISEMENT
  • Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
  • 2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Ya dai gaje Farfesa Mahmood Yakubu, wanda wa’adinsa na shekaru 10 ya kare a matsayin shugaban INEC a ranar Talata.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

A taron majalsar zartarwar, Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa zabinsa na Amupitan ya yi ta’allaka ne a kan rashin nuna son kai na siyasa, gaskiya da kyakkyawan tarihinsa.

 

Mambobin majalisar, ciki har da shugabanni na yanzu da na baya, sun amince da nadin, suna bayyana Farfesa Amupitan a matsayin mutum mai gaskiya. Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya ce tarihin Amupitan na ciki da kwazo da adalci da kwarewa da hidimar kasa.

 

Bayan amincewar majalisar, ana sa ran shugaba zai mika sunan Amupitan zuwa majalisar dattawa don tantancewa da tabbatarwa bisa ga tsarin kundin mulkin Nijeriya.

 

Farfesa Amupitan, mai shekaru 58, dan asalin kauyen Ayetoro Gbede a cikin karamar hukumar Ijumu ta Jihar Kogi. Ya kasance farfesa ne a bangaren shari’a a jami’ar Jos ta Jihar Filato, shi ne mataimakin shugaban jami’a. Haka kuma, shi ne shugaban kwamitin majalisar gudanarwa na jami’ar Joseph Ayo Babalola da ke Jihar Osun.

 

Jam’iyyun siyasa sun yi kira ga Farfesa Amupitan da ya dawo da amincewar jama’a ga tsarin zaben Nijeriya ta hanyar gaskiya, rashin son zuciya, da gyara tsarin hukumar.

 

A martani jam’iyyar hadaka ta ADC ta gargadi sabon shugaban INEC, da ya kasance mai biyayya ga mutanen Nijeriya ba wai ga bukatun siyasa ba. Wannan na zuwa ne yayin da jam’iyyar PDP ta yi kira gare shi da ya fifita tsarkake tsarin zabe ta hanyar sauye-sauye domin dawo da amincewar jama’a ga hukumar.

 

Sai dai jam’iyyar APC mai mulki ta nuna gamsuwa da nadin Amupitan, inda ta bayyana cewa an zabe shi ne bisa cancanta kuma dole ne ya nuna adalci, gaskiya, da himma wajen ci gaba da aiwatar da gyare-gyaren zabe da ake yi.

 

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, sakataran yada labarai na kasa na jam’iyyar ADC, Bolaji Abdullahi, ya yi kira ga sabon shugaban INEC da ya sanya aminci ga mutanen Nijeriya maimakon na gwamnatin APC mai mulki. Abdullahi ya jaddada bukatar dawo da amincewar jama’a ga tsarin zaben kasa, yana mai cewa jam’iyyar hadaka ta shirya bai wa sabon shugaban INEC hadin kai. Jam’iyyar tana fatan Amupitan zai yi aiki mafi kyau a zaben 2027.

A halin da ake ciki, mataimakin shugaban matasa na kasa na jam’iyyar PDP, Timothy Osadolor, ya yi kira ga Amupitan da ya aiwatar da gyare-gyare da za su karfafa dimokuradiyyar Nijeriya.

A bangarensa, darakta halda da jama’a na APC, Bala Ibrahim, ya yaba da nadin, inda ya bayyana cewa nadin Farfesa Amupitan ya dogara ne kan cancanta.

Sai dai kuma ‘yan adawa sun kafa wa sabon shugaban INEC sharudda kan gyaran zabe da gaskiya da bin doka yayin da ya shiga ofisi.

A martaninsa kan nada Amupitan, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi, da jam’iyyar NNPP sun yi fatan alheri tare yin kira a gare shi ya yi taka tsantsan kan nadin da aka yi masa.

Sakataren yada labarai na kasa na Jam’iyyar NNPP, Ladipo Johnson, ya yi kira ga Amupitan da ya gina jagorancinsa a kan bin doka kuma ya dauki darasi daga kurakuran da aka samu a zaben 2023.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
INEC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe
  • Sulaiman
    GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara
  • Sulaiman
    Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026
  • Sulaiman
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.