• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mai Yiwuwa Ne Matakan Sin Na Iya Maida Komadar Tattalin Arzikin Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Mai Yiwuwa Ne Matakan Sin Na Iya Maida Komadar Tattalin Arzikin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da tattalin arzikin duniya ke cikin halin rashin tabbas a sakamakon tarin matsalolin da suka yi masa dabaibayi, hakika, tattalin arzikin duniya yana fama da wahalhalu a wannan lokaci.

Koda yake, mai yiwuwa ne tattalin arzikin duniyar zai iya samun sassauci gami da farfadowa a sakamakon wasu jerin matakan da kasa ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya ke dauka, wadanda suka shafi matakan daidaita yanayin tattalin arzikin kasar na cikin gida kuma ka iya yin tasiri ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya.

  • Jakadan Sin A Saliyo Ya Halarci Taron Karawa Juna Sani Tsakanin Ofishin Jakadancinsa Da Kungiyoyin Sada Zumunta Ta Kasashen Biyu

A karshen wannan mako ne, babban bankin duniya ya fitar da sabon rahoto kan tattalin arzikin kasar Sin, inda mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian ya yi tsokaci kan wannan batu, inda ya bayyana cewa, yayin da ake fuskantar kalubale daban-daban a cikin gida da kuma waje, tattalin arzikin kasar Sin zai iya tabbatar da daidaito da samun ci gaba na dogon lokaci da ma ba da kwarin gwiwar daidaitawa da farfado da tattalin arzikin duniya.

Sabon rahoton tattalin arzikin Sin din da babban bankin duniya ya fitar ya nuna cewa, a cikin rubu’in farko na wannan shekara, tattalin arzikin kasar Sin ya samu bunkasa sosai. Biyo bayan wasu tsare-tsare da matakai na daidaita tattalin arziki, ana sa ran saurin bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin ya sake dawowa a cikin rubu’i na biyu na wannan shekara.

Ita ma babbar hukumar kwastom ta kasar Sin GAC, ta sanar da cewa, a watanni biyar din farko na shekarar 2022, hada-hadar cinikayyar kasashen waje na kasar Sin ya samu karin kashi 8.3 bisa 100, idan an kwatanta da makamancin lokacin bara inda adadin ya karu zuwa RMB yuan triliyan 16.04. Ta fannin dalar Amurka kuwa, jimillar cinikayyar kasashen wajen ya kai dala triliyan 2.51 a cikin watannin biyar, inda ya karu da kashi 10.3 a bisa na makamancin lokacin bara.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

A cikin wannan wa’adi kuma, cinikayyar kasar Sin da manyan abokan huldar kasuwanci uku, wato kungiyar kasashen kudu maso gabashin Asiya, da kungiyar tarayyar Turai, da kuma Amurka, ya karu da kashi 8.1 bisa 100, da kashi 7 bisa 100, da kuma kashi 10.1 bisa 100, idan an kwatanta da shekarar da ta gabata.
Daga watan Janairu zuwa Mayu, huldar kasuwancin Sin da kasashen dake bin shawarar “ziri daya da hanya daya”, ya karu zuwa kashi 16.8 bisa 100 a bisa na makamancin lokacin bara, inda ya karu zuwa RMB yuan triliyan 5.11. Abin da ya bayyana a fili shi ne, an samu farfadowar ne bayan da gwamnatin kasar Sin ta dauki matakan tallafawa kamfanonin kasashen ketare, wajen rage musu wahalhalu a sakamakon barkewar annobar COVID-19 a cikin gida, da kuma rashin tabbas a yanayin tattalin arzikin kasashen ketare.

A cewar Li Kuiwen, jami’in babbar hukumar GAC, kasar Sin ta bullo da wasu jerin matakan daidaita yanayin tattalin arziki, da kuma inganta yanayin kasuwancin waje a cikin wannan shekarar, matakan wadanda dama an yi tsammanin za su taimaka wajen saurin farfadowar tattalin arzikin da zarar suka fara aiki.

Ko shakka babu, wadannan wasu alamu ne a bayyane dake kara nuna tasirin matakan da kasar Sin ke dauka wajen daidaita yanayin tattalin arzikinta wadanda ba kawai suna amfanawa kasar kadai ba ne, har ma suna kara samar da tabbaci ga ci gaban tattalin arzikin duniya. (Ahmad Fagam)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyar ‘Yan Ta’adda Ta Ansaru Ta Ce Ba Ita Ta Kai Hari Kan Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ba

Next Post

‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga 1 Da Dakile Wani Hari Kan Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

13 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

14 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

16 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

16 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

18 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

20 hours ago
Next Post
‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga 1 Da Dakile Wani Hari Kan Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga 1 Da Dakile Wani Hari Kan Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.