• Leadership Hausa
Friday, August 19, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Daga Birnin Sin

Mai Yiwuwa Ne Matakan Sin Na Iya Maida Komadar Tattalin Arzikin Duniya

by CMG Hausa
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Mai Yiwuwa Ne Matakan Sin Na Iya Maida Komadar Tattalin Arzikin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da tattalin arzikin duniya ke cikin halin rashin tabbas a sakamakon tarin matsalolin da suka yi masa dabaibayi, hakika, tattalin arzikin duniya yana fama da wahalhalu a wannan lokaci.

Koda yake, mai yiwuwa ne tattalin arzikin duniyar zai iya samun sassauci gami da farfadowa a sakamakon wasu jerin matakan da kasa ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya ke dauka, wadanda suka shafi matakan daidaita yanayin tattalin arzikin kasar na cikin gida kuma ka iya yin tasiri ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya.

  • Jakadan Sin A Saliyo Ya Halarci Taron Karawa Juna Sani Tsakanin Ofishin Jakadancinsa Da Kungiyoyin Sada Zumunta Ta Kasashen Biyu

A karshen wannan mako ne, babban bankin duniya ya fitar da sabon rahoto kan tattalin arzikin kasar Sin, inda mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian ya yi tsokaci kan wannan batu, inda ya bayyana cewa, yayin da ake fuskantar kalubale daban-daban a cikin gida da kuma waje, tattalin arzikin kasar Sin zai iya tabbatar da daidaito da samun ci gaba na dogon lokaci da ma ba da kwarin gwiwar daidaitawa da farfado da tattalin arzikin duniya.

Sabon rahoton tattalin arzikin Sin din da babban bankin duniya ya fitar ya nuna cewa, a cikin rubu’in farko na wannan shekara, tattalin arzikin kasar Sin ya samu bunkasa sosai. Biyo bayan wasu tsare-tsare da matakai na daidaita tattalin arziki, ana sa ran saurin bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin ya sake dawowa a cikin rubu’i na biyu na wannan shekara.

Ita ma babbar hukumar kwastom ta kasar Sin GAC, ta sanar da cewa, a watanni biyar din farko na shekarar 2022, hada-hadar cinikayyar kasashen waje na kasar Sin ya samu karin kashi 8.3 bisa 100, idan an kwatanta da makamancin lokacin bara inda adadin ya karu zuwa RMB yuan triliyan 16.04. Ta fannin dalar Amurka kuwa, jimillar cinikayyar kasashen wajen ya kai dala triliyan 2.51 a cikin watannin biyar, inda ya karu da kashi 10.3 a bisa na makamancin lokacin bara.

Labarai Masu Nasaba

Ana Shirin Fadada Layukan Dogo Na Karkashin Kasa Dake Birnin Beijing

Xi Jinping Ya Yi Rangadin Aiki A Birnin Shenyang

A cikin wannan wa’adi kuma, cinikayyar kasar Sin da manyan abokan huldar kasuwanci uku, wato kungiyar kasashen kudu maso gabashin Asiya, da kungiyar tarayyar Turai, da kuma Amurka, ya karu da kashi 8.1 bisa 100, da kashi 7 bisa 100, da kuma kashi 10.1 bisa 100, idan an kwatanta da shekarar da ta gabata.
Daga watan Janairu zuwa Mayu, huldar kasuwancin Sin da kasashen dake bin shawarar “ziri daya da hanya daya”, ya karu zuwa kashi 16.8 bisa 100 a bisa na makamancin lokacin bara, inda ya karu zuwa RMB yuan triliyan 5.11. Abin da ya bayyana a fili shi ne, an samu farfadowar ne bayan da gwamnatin kasar Sin ta dauki matakan tallafawa kamfanonin kasashen ketare, wajen rage musu wahalhalu a sakamakon barkewar annobar COVID-19 a cikin gida, da kuma rashin tabbas a yanayin tattalin arzikin kasashen ketare.

A cewar Li Kuiwen, jami’in babbar hukumar GAC, kasar Sin ta bullo da wasu jerin matakan daidaita yanayin tattalin arziki, da kuma inganta yanayin kasuwancin waje a cikin wannan shekarar, matakan wadanda dama an yi tsammanin za su taimaka wajen saurin farfadowar tattalin arzikin da zarar suka fara aiki.

Ko shakka babu, wadannan wasu alamu ne a bayyane dake kara nuna tasirin matakan da kasar Sin ke dauka wajen daidaita yanayin tattalin arzikinta wadanda ba kawai suna amfanawa kasar kadai ba ne, har ma suna kara samar da tabbaci ga ci gaban tattalin arzikin duniya. (Ahmad Fagam)

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyar ‘Yan Ta’adda Ta Ansaru Ta Ce Ba Ita Ta Kai Hari Kan Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ba

Next Post

‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga 1 Da Dakile Wani Hari Kan Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Related

Ana Shirin Fadada Layukan Dogo Na Karkashin Kasa Dake Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

Ana Shirin Fadada Layukan Dogo Na Karkashin Kasa Dake Birnin Beijing

17 hours ago
Xi Jinping Ya Yi Rangadin Aiki A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Yi Rangadin Aiki A Birnin Shenyang

18 hours ago
Babu Nasara Ga ’Yan Awaren Taiwan
Daga Birnin Sin

Babu Nasara Ga ’Yan Awaren Taiwan

19 hours ago
Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Ra’ayin Blinken Kan Batun “Tarkon Bashi Na Kasar Sin”
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Ra’ayin Blinken Kan Batun “Tarkon Bashi Na Kasar Sin”

20 hours ago
Sin: Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Haifar Da Sakamako Mai Kyau Da Fa’ida
Daga Birnin Sin

Sin: Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Haifar Da Sakamako Mai Kyau Da Fa’ida

21 hours ago
Ana Kulle Kaya A Manyan Shagunan Zamani Da Makulli A Amurka
Daga Birnin Sin

Ana Kulle Kaya A Manyan Shagunan Zamani Da Makulli A Amurka

22 hours ago
Next Post
‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga 1 Da Dakile Wani Hari Kan Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga 1 Da Dakile Wani Hari Kan Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

LABARAI MASU NASABA

Dambu Ya Yi Sanadin Mutuwar `Yan’uwa 7 A Zamfara

Dambu Ya Yi Sanadin Mutuwar `Yan’uwa 7 A Zamfara

August 19, 2022
Buhari Ya Ci Alwashin Kawo Karshen Lalacewar Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasa

Gwamnatin Nijeriya Na Kashe Naira Biliyan N18.397 Kullum A Bangaren Tallafin Mai

August 19, 2022
Yadda Aka Sace Kwamishina A Nasarawa

Yadda Aka Sace Kwamishina A Nasarawa

August 19, 2022
Nadin Kwamishinoni A Kano: Kar A Yi Kitso Da Kwarkwata

Nadin Kwamishinoni A Kano: Kar A Yi Kitso Da Kwarkwata

August 19, 2022
Da Dumi-Duminsa: NBC Ta Soke Lasisin Tashoshin AIT, Silverbird TV Da Wasu 50

Da Dumi-Duminsa: NBC Ta Soke Lasisin Tashoshin AIT, Silverbird TV Da Wasu 50

August 19, 2022
srilanka

Darussa Daga Gwagwarmayar Kasar Sri Lanka (Nazari)

August 19, 2022
Goro

Goron Jumu’a

August 19, 2022
Nunez Ya Jika Wa Liverpool Aiki

Nunez Ya Jika Wa Liverpool Aiki

August 19, 2022
Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

August 19, 2022
Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

August 19, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.