• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalaman Kiyayya Da Yada Su Na Haddasa Rikici Tsakanin Al`umma

by Mustapha Ibrahim
3 years ago
Kiyayya

Kalamai dai ma`anarsu, furuci ne da baki, na wasu maganganu kiyayya kuma su ne, kishiyar soyayya, ko kauna, idan ba ka san kiyayya ba, to ana nufun kishiyar kyauna, ko so, misali kishiyar zaki shi ne daci, to wannan kalma mai harufa bakwai kacal, yin ta ga wani mutum ko wata al`umma, ta siyasa ko ta kabila, kalma ce mai nauyi, da ke haddasa rigingimu da tashin hankali a duniya.

Domin kowa duk inda aka yi wannan kalama, to ba shakka da zarar an yada, to abu ne, da ke kawo matsala a kowace irin kasa a duniya, kamar yadda labaran karya da yada jita-jita ke hadasa wa.

  • Dalilin Haramta Wa ‘Yan Adaidaita Sahu Bin Manyan Tituna – Gwamnatin Kano
  • An Tsinci Gawar Wani Dan Kasuwa Mai Shekaru 37 A Otel A Jihar Bauchi

Dan haka ne ma, za ka ga cewa, misali abu na farko da ake karantar da dan jarida tun a matakin farko, shi ne iya bakinsa ta hanyar kauce wa kalamai na bata wani mutum ko wata kabila ko kungiyar wasu mutane ko mabiya wani addini da suka yi imani da shi.

Idan ban manta ba, kuma in na fahimta a karatuna na jarida a tsakanin makarantar koyan aikin jarida da ke karkashin hukumar AME a kano, da karatuna na BUK da ni yi karatun jarida cikin cokali, a shekarun da suka wuce, akwai dokoki da dama a darasin da ake cewa “PRESS LAW” ko kuma “Communication Law” a cikin wannan darasi akwai maganar wani abu da ake ce wa “Defamation” wanda ke nufin ka da ka bata sunan mutum, ko aibata shi da daraja, ko kimarsa ta zube. Wannan kuma na san ana karantar da ‘yan jarida ne bisa la`akari da yadda aikinsu na rubutu a jarida ko a karanta a rediyo da talabijin,da sauran kafafn yada labarai.

Wannan kuwa dole a ba shi horan iya magana don kauce wa kalaman kiyayya ko yada su, Kamar yadda yake faruwa a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

Kyakkyawan misali na illar kalaman kiyayya da yada su da tarihin duniya ba zai manta da shi ba, shi da ya faru a daya daga cikin kasashen Afrika wato kasar Ruwanda a shekara ta1988, tsakanin kabilar Hutu da Tutsi, inda aka kasha dubban muta ne, wanda ba su ji ba ba su gani ba, wanda an ce ko a rana daya an kashe mutum dubu 100 wannan fa ba wani abu ba ne ya jawo shi ba, sai kalaman kiyayya da yada su.

An ce, Kalmar ta faro ne daga wani mutum na cewa AKASHE KYANKYASAI ita ce aka yi amfani da ita a tsakanin kabilar Hutu da Tutsi manyan kabilu ne a kasar masu rinjaye da marasa rinjaye a cikinsu bayan harbo jirgin shugaban kasa da ya fito daga daya kabilar ta Ruwanda, da aka yi a kasar duk dai kalaman kiyayya ne da yada su ta jawo wa kasar Ruwanda wannan masifa, wanda yanzu ya wuce ya zama tarihi da ba a fatan irinsa ko maimaita shi a ko’ina cikin duniya.

Akwai bukatar ya zama darasi ga ‘yan Nijeriya musamam ‘yan siyasa da na ji a kwananan wata jami`a a ofishin jakadancin Birrtaniya ta yi kashedi na hana me yin wannan shiga kasarta kalamun da ka iya kawo wa dimakaradiyya cikas a Najeriya.

Haka kuma idan ka koma can baya a tarihi za ka ga cewa an yi yake-yake a duniya musali idan ka dau tarihi na Larabawa da za ka ga cewa an yi yake- yake tun kafun zuwan addin Musulunci, wanda ba wani abu ba ne ya hadasa irin wadanan yake-yake sai kalamai na kiyayya da yada shi a tsakanin mawaka da masana fanin ke cewa mawakan jahiliya, da sauransu inka dawo baya kadan za ka ga cewa an yi yaki tsakanin kasar Amurka da kawayenta wajan yakar kasar Iraki idan ka karanta tarihin wannan yaki da aka fara a 1991 za ka ga asalin wannan yaki a faru ne daga kalamai na rashin fahimtar juna a tsakanin su wanda za ka iya kiransa da kalaman kiyayya da yada shi.

Kafin mu dawo gida Nijeriya dan ba da misali da abubuwa na tashin hankali da suka faru a kasashe wani abu da za ka iya kira da kalaman kiyayya ne ya hadasa su a kasashen Turai, Duniya ba za ta manta da abun da aka yi ba na yakin duniya na daya da yakin duniya na biyu ba, ko ba a cema kalaman kiyayya ne suka hadasa wannan ba to ba ka ce ko kalaman soyayya ba ne, ko kauna ce ta hada sa yakin duniya na daya da na biyu ba, in ko ba haka ba ne ya zama kalaman kiyayya Ke nan.

Ka dubi abubuwan da suka faru na siyasar duniya a tsakanin kasashen yammacin Turai da tarayar Sobiyat, tsakanin yan kwamnis da yan jari huja na cacar-baka na shekara da shekaru, da ya kawo karshe bayan rushewar tarayar Sobiyat, da sauransu. Ka da mu manta da wata kalma da ake kira da turanci Crusade tana cikin tarihi duniya mana dadi, har yanzu ba mai san tu na ta ko amfani da ita a duniya.

Tarihin Nijeriya ba zai kammala ba sai ka sa maganar yakin Biyafara, a kano sai kasa tarihin yakin mai tatsine, da sauran rigingimu na siyasar NEPU da NPC wanda ya gangaro har zuwa maganar santsi tabo duk wadanan da aka yi ba sunansu zaman lafiya ba duk da sun zama tarihi amma an san ba kalaman yabo ko kauna ce ya kawo wadanan rigingimu ba, kishiyar kalaman so ne da kauna ya kawo wadanan rigingimu.

Wani musali na kwananan shi ne yanzu haka wata koto a kasar nan, na tuhumar wani matashi dan asalin jahar jigawa, mai suna Aminu Adamu kan zargin kalaman batanci da yada kiyayya ga uwargidan shugaban kasa Muhammadu Buhari a kafafan sada zumunta da aka zargi matashin da yin hakan, kuma wani abu mai kama da haka ya faru a Kaduna tsakanin wani malami da wani dan siyasa kuma tsowan soja daya zargi malamun da kalaman kiyayya a kansa inda sai a gaban koto aka warware wannan matsala tsakanin wani malami da wani tsohon soja a Kaduna kamar yadda kafafan yada labarai suka ba da labia a lokacin.

Abubuwa da daman a rashin fahimtar juna na da yawa wanda kalaman kiyayya da yadasu ke hadasawa ko rikicin gida da ake yi tsakanin kishiya da kishiya ko makoci da makoci ko aboki da aboki da direba da direba akan hanya da makamantansu ba kalaman suyayya ne suke hada su ba.

Kuma wannan kalma ta kiyayya kishiyar soyayya ta fi zafi a yanzu haka musammam ga yan siyasa wanda kuma babbar masifa ce da ya kamata a kauce ma a wannan lokaci da mu a Najeriya ake sauran kwanaki kasa da 90 dan shiga runfunan zaban shugaban kasa, da sanatoci, wakilan tarayya, gwamnoni da yan majalisar jaha a tarayar Nijeriya.

Duk dai wannan kalma ta kiyayya ba ta da tasiri sai an yada ta a kafafan yada labarai wanda kuma yanzu haka babban kalubalan da ke gaban mu shi ne yanzu na kafofun sada zumunta na zamani da kuma wasu gidajen rediyo da sauran wasu kafafn yada labarai wadanda ko dai basu horo na aikin yada labarai, ko kuma san zuciya ya danne huran da karatunsu na ba sa aiki da shi, kuma wannan babban kalubale ne, na a guji wadanan kalamai na yada kiyayya da yin ta wannan kuma ya hada da wuraran tarowa da yin lakcoci ko huduba, a masalatai da ma jami`u a guji yin kalaman kiyayya da kuma yada su ta kafafan yada labarai, domun su ne kanwa uwar gami wajen ya ya ta abun da zai kawo zaman lafiya ko akasain ha ka wato kishiyar haka a Nijeriya dama duniya baki daya dan haka dole a yi hatara!

Wata na siha da zan karkare wannan rubutu da ita ita ce nasihar da daya daga cikin malamai a wani lokacin a wata hira muka yi da shi a kwanakin baya inda Sheikh Dr Bashir Aliyu Umar, OON ya yi na cewa kalaman kiyayya da yadashi da jita jita addini bai yadda da shi ba, inda ya ce wajibi ne su limamai su guji yada kalamai wadanda za su tunzura jama`a a Mambarurunsu na huduba inda ya ce ko da mutum ba dai dai ya ke ba to munin aikin za a fada ba a nu na masa kiyayya ba, domun anga irin masifun da irin wadanan abubuwa su ka jawowa duniya dan haka wajibi ne a isar da sako cikin hikima kamar yadda aka koyar mana a lidafun Allah mai tsarki, kuma a guji yada labaran karya ko yada kiyayya karya, da jita jita ba su taba zama alkairi a rayuwa.

Mustapha Ibrahim, Wakilin LEADERSHIP Hausa ne, ya rubuto daga Kano

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Next Post
Da Farko Na Ji Kamar Ba Zan Iya Ci Gaba Da Harkar Fim Ba —Umar Faruk

Da Farko Na Ji Kamar Ba Zan Iya Ci Gaba Da Harkar Fim Ba —Umar Faruk

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.