A karo na 8 a jere, kasar Sin na karbar bakuncin taron baje koli na kasa da kasa na kayayyakin da ake shigo da su kasar (CIIE).
Kamar yadda muka sani, baje koli ko a cikin gida ko a waje, wata dama ce ga ’yan kasuwa daga sassa daban-daban na haduwa da kulla dangantaka da kara bude ido da samun ilimi, baya ga sayar da kayayyaki. Sanin kowa ne cewa, kasar Sin babbar kasuwa ce, kuma galibin kasashe da ’yan kasuwarsu na hankoron shigowa kasar domin amfana da katafariyar kasuwarta.
Sabanin yadda muke gani yanzu a duniya, wato yadda ake sanya takunkumai da kariya domin kawo tsaiko ga tsarin ayyukan masana’antu da samar da kayayyaki a duniya, kasar Sin tana kara bude kofarta da maraba da karin kamfanonin kasashen waje su shigo su ci gajiyar ci gaban da ta samu da kara habaka harkokinsu na kasuwanci domin a samu moriyar juna har a kai ga gina al’umma mai makoma ta bai daya ga dukkan bil adama.
Idan muka waiwaya, a baya bayan nan, Sin ta bayyana matakin soke haraji da kashi 100 bisa 100 a kan kayayyakin kasashen Afrika 53 da suka kulla huldar jakadanci da ita. Wannan na nufin, tana kara bude kofarta ga kasashen na Afrika, domin su kara shigo da kayayyakinsu kasar.
A bana, an fadada wuraren nune-nunen hajojin kasashen Afrika, kana, adadin kamfanoni daga kasashen Afrika ya karu da kaso 80 bisa dari, idan aka kwatanta da na bara. To idan muka hada duka wadannan, za mu ga cewa, CIIE ya zama wani karin tagomashi ga kasashen. Kasar Sin ta sake ba kasashen Afrika dama ta kyautata hanyar kawo hajajojinsu da cudanya da ’yan kasuwa da nazarin bangarorin da za su fi amfanar su da kuma mu’amala da Sinawa, har da ma sauran jama’ar kasa da kasa mahalarta bikin. Don haka CIIE ya amsa sunansa na katafaren dandali na karawa kasashe kwarin gwiwar tallata kayayyakinsu ga daukacin kasashen duniya.( Fa’iza Mustapha)














