• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kasa Ita Ce Ke Dinke Baraka Ba Kawo Rarrabuwar Kawuna Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Babbar Kasa Ita Ce Ke Dinke Baraka Ba Kawo Rarrabuwar Kawuna Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin taron Shangri-La, da ministocin tsaron kasashen yankin Asiya ke muhawara kan muhimman kalubalen tsaro da yankin ke fuskanta tare da gabatar da dabarun shawo kansu, sakataren tsaron Amurka Lloyd J. Austin III ya tabo wasu batutuwa da suka shafi kasar Sin.

Ya ce a baya-bayan nan, ana samun matsi daga rundunar sojin kasar Sin a yankin tekun kudancin kasar. Sai dai rahotanni sun nuna cewa, sama da jiragen ruwa 100,000 ne ke zirga-zirga a tekun a kowacce shekara, kuma babu wanda ya taba fuskantar barazana.

  • Sin Ta Gudanar Da Ayyukan Nazarin Kayan Tarihi Fiye Da 8800 A Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Tabbas kasar Sin ba ta takalar fada, sai dai mayar da martani idan aka takale ta. Don haka, duk wani wanda zai yi korafi game da fuskantar barazana daga rundunar sojin kasar Sin, to takalarta ya yi ko keta dokokin, domin Sin ba ta daukar wargi.

Ya kara da cewa, ba su sauya matsayarsu kan manufar kasar Sin daya tak a duniya da yarjejeniyoyin da kasashen biyu suka cimma ba, amma kuma za su ci gaba da taimakawa Taiwan zama mai dogaro da kanta a fannin tsaron kai.

Shin me hakan ke nufi? Duk wanda ya amince da ka’idar kasancewar kasar Sin daya tak da gaske, ya san cewa bai halarta ya yi wata hulda ta kai tsaye da yankin Taiwan ba.

Labarai Masu Nasaba

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

Ikirarin taimakawa Taiwan ta fuskar tsaro, ya nuna karara cewa, Amurka na goyon bayan masu neman ballewar yankin, abun da Sin ta sha nanata cewa ba mai yuwuwa ba ne. Kuma a matsayinta na mai wakiltar baki daya Jamhuriyar kasar Sin, batun tsaron Taiwan, hakki ne na kasar Sin, ba wata kasar waje ba.

Amurka na ikirarin ta damu da tsaron yankin Asiya. Idan har da gaske take, ganin cewa dukkan kasashen yankin na da cikakken iko da yankunansu, kamata ya yi a yi la’akari da bukatun da damuwar kowacce kasa.

Kamata ya yi a girmama ’yancin kasashen yankin da hanyoyin ci gaba ko tafiyar da mulki ko na tabbatar da tsaro da suka zabarwa kansu. Bai dace wata kasa ta yi kokarin kakkaba tsarinta a kan wata ba, domin mai daki shi ya san inda yake masa yoyo.

Har ila yau, ya ce matsayin babbar kasa na nufin daukar babbar nauyi. Sai dai sam wannan suna ba ta dace da Amurka ba. Babbar kasa ita ta san ya kamata, ita ke dinke baraka idan ta bullo, ba rura wutar rikici ba, ita ke hade kan al’umma ba kawo rarrabuwar kawuna ba. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lalacewar Babbar Hanyar Lantarki Ta Kasa Na Tabbatar Da Gazawar Nijeriya A Komai – Atiku

Next Post

Yang Jiechi Ya Gana Da Mai Taimakawa Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaron Kasa

Related

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

12 minutes ago
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

1 hour ago
An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

2 hours ago
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

11 hours ago
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

20 hours ago
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Daga Birnin Sin

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

22 hours ago
Next Post
Yang Jiechi Ya Gana Da Mai Taimakawa Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaron Kasa

Yang Jiechi Ya Gana Da Mai Taimakawa Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

August 7, 2025
Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

August 7, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

An Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 30 A Wani Harin Jirgin Sama A Wurin Daurin Aure A Zamfara

August 7, 2025
An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

August 7, 2025
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

August 7, 2025
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

August 7, 2025
Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi

August 7, 2025
Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don ÆŠaukar Nunez Daga Liverpool

Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don ÆŠaukar Nunez Daga Liverpool

August 7, 2025
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.