• Leadership Hausa
Thursday, August 11, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Daga Birnin Sin

Babbar Kasa Ita Ce Ke Dinke Baraka Ba Kawo Rarrabuwar Kawuna Ba

by CMG Hausa
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Babbar Kasa Ita Ce Ke Dinke Baraka Ba Kawo Rarrabuwar Kawuna Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin taron Shangri-La, da ministocin tsaron kasashen yankin Asiya ke muhawara kan muhimman kalubalen tsaro da yankin ke fuskanta tare da gabatar da dabarun shawo kansu, sakataren tsaron Amurka Lloyd J. Austin III ya tabo wasu batutuwa da suka shafi kasar Sin.

Ya ce a baya-bayan nan, ana samun matsi daga rundunar sojin kasar Sin a yankin tekun kudancin kasar. Sai dai rahotanni sun nuna cewa, sama da jiragen ruwa 100,000 ne ke zirga-zirga a tekun a kowacce shekara, kuma babu wanda ya taba fuskantar barazana.

  • Sin Ta Gudanar Da Ayyukan Nazarin Kayan Tarihi Fiye Da 8800 A Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Tabbas kasar Sin ba ta takalar fada, sai dai mayar da martani idan aka takale ta. Don haka, duk wani wanda zai yi korafi game da fuskantar barazana daga rundunar sojin kasar Sin, to takalarta ya yi ko keta dokokin, domin Sin ba ta daukar wargi.

Ya kara da cewa, ba su sauya matsayarsu kan manufar kasar Sin daya tak a duniya da yarjejeniyoyin da kasashen biyu suka cimma ba, amma kuma za su ci gaba da taimakawa Taiwan zama mai dogaro da kanta a fannin tsaron kai.

Shin me hakan ke nufi? Duk wanda ya amince da ka’idar kasancewar kasar Sin daya tak da gaske, ya san cewa bai halarta ya yi wata hulda ta kai tsaye da yankin Taiwan ba.

Labarai Masu Nasaba

Wang Wenbin: Hannuwan ‘Yan Siyasar Amurka Da “‘Yan Ina Da Yaki” Na Jike Da Jinin Al’ummun Gabas Ta Tsakiya

Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Ikirarin taimakawa Taiwan ta fuskar tsaro, ya nuna karara cewa, Amurka na goyon bayan masu neman ballewar yankin, abun da Sin ta sha nanata cewa ba mai yuwuwa ba ne. Kuma a matsayinta na mai wakiltar baki daya Jamhuriyar kasar Sin, batun tsaron Taiwan, hakki ne na kasar Sin, ba wata kasar waje ba.

Amurka na ikirarin ta damu da tsaron yankin Asiya. Idan har da gaske take, ganin cewa dukkan kasashen yankin na da cikakken iko da yankunansu, kamata ya yi a yi la’akari da bukatun da damuwar kowacce kasa.

Kamata ya yi a girmama ’yancin kasashen yankin da hanyoyin ci gaba ko tafiyar da mulki ko na tabbatar da tsaro da suka zabarwa kansu. Bai dace wata kasa ta yi kokarin kakkaba tsarinta a kan wata ba, domin mai daki shi ya san inda yake masa yoyo.

Har ila yau, ya ce matsayin babbar kasa na nufin daukar babbar nauyi. Sai dai sam wannan suna ba ta dace da Amurka ba. Babbar kasa ita ta san ya kamata, ita ke dinke baraka idan ta bullo, ba rura wutar rikici ba, ita ke hade kan al’umma ba kawo rarrabuwar kawuna ba. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lalacewar Babbar Hanyar Lantarki Ta Kasa Na Tabbatar Da Gazawar Nijeriya A Komai – Atiku

Next Post

Yang Jiechi Ya Gana Da Mai Taimakawa Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaron Kasa

Related

Wang Wenbin: Hannuwan ‘Yan Siyasar Amurka Da “‘Yan Ina Da Yaki” Na Jike Da Jinin Al’ummun Gabas Ta Tsakiya
Daga Birnin Sin

Wang Wenbin: Hannuwan ‘Yan Siyasar Amurka Da “‘Yan Ina Da Yaki” Na Jike Da Jinin Al’ummun Gabas Ta Tsakiya

24 mins ago
Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne
Daga Birnin Sin

Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

1 hour ago
Tarihi Baya Mantuwa
Daga Birnin Sin

Tarihi Baya Mantuwa

2 hours ago
Yawan Injuna Da Kasar Sin Ta Fitar Da Su Zuwa Ketare A Farkon Rabin Bana Ya Karu Da Kashi 10.41%
Daga Birnin Sin

Yawan Injuna Da Kasar Sin Ta Fitar Da Su Zuwa Ketare A Farkon Rabin Bana Ya Karu Da Kashi 10.41%

3 hours ago
Ya Kamata A Bar Sinawa Su Yanke Shawara Kan Al’amuran Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Bar Sinawa Su Yanke Shawara Kan Al’amuran Kasar Sin

4 hours ago
Kotu Ta Amince Da Bayar Da Belin Wanda Ya Yi Garkuwa Da Yayarsa A Zariya
Daga Birnin Sin

Kotu Ta Amince Da Bayar Da Belin Wanda Ya Yi Garkuwa Da Yayarsa A Zariya

7 hours ago
Next Post
Yang Jiechi Ya Gana Da Mai Taimakawa Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaron Kasa

Yang Jiechi Ya Gana Da Mai Taimakawa Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Wang Wenbin: Hannuwan ‘Yan Siyasar Amurka Da “‘Yan Ina Da Yaki” Na Jike Da Jinin Al’ummun Gabas Ta Tsakiya

Wang Wenbin: Hannuwan ‘Yan Siyasar Amurka Da “‘Yan Ina Da Yaki” Na Jike Da Jinin Al’ummun Gabas Ta Tsakiya

August 11, 2022
Dariye Zai Tsaya Takarar Sanata A Filato Bayan Yi Masa Afuwa Daga Gidan Yari

Dariye Zai Tsaya Takarar Sanata A Filato Bayan Yi Masa Afuwa Daga Gidan Yari

August 11, 2022
Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

August 11, 2022
Tarihi Baya Mantuwa

Tarihi Baya Mantuwa

August 11, 2022
Jerin Sunayen Sabbin Ministocin Da Buhari Ya Aike Wa Majalisar Dattijai Ta Tantance Su

DA DUMI-DUMI: Buhari Ya Gana Da Iyalan Fasinjojin Jirgin Da Aka Sace A Kaduna

August 11, 2022
Yawan Injuna Da Kasar Sin Ta Fitar Da Su Zuwa Ketare A Farkon Rabin Bana Ya Karu Da Kashi 10.41%

Yawan Injuna Da Kasar Sin Ta Fitar Da Su Zuwa Ketare A Farkon Rabin Bana Ya Karu Da Kashi 10.41%

August 11, 2022
Ya Kamata A Bar Sinawa Su Yanke Shawara Kan Al’amuran Kasar Sin

Ya Kamata A Bar Sinawa Su Yanke Shawara Kan Al’amuran Kasar Sin

August 11, 2022
Kotu Ta Daure Fasto Da Wasu 2 Kan Zargin Yin Sojan Gona Da Sunan Jami’an EFCC, ICPC A Akwa Ibom

Kotu Ta Daure Fasto Da Wasu 2 Kan Zargin Yin Sojan Gona Da Sunan Jami’an EFCC, ICPC A Akwa Ibom

August 11, 2022
Matukar Nijeriya Ba Ta Sanya Idanu Kan Kudaden Shigarta Ba Akwai Matsala —Bankin Duniya

Matukar Nijeriya Ba Ta Sanya Idanu Kan Kudaden Shigarta Ba Akwai Matsala —Bankin Duniya

August 11, 2022
Gwamnatin Gombe Zata Fadada Hanyoyin Ture, Bakasi Zuwa Gelengu

Gwamnatin Gombe Zata Fadada Hanyoyin Ture, Bakasi Zuwa Gelengu

August 11, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.