ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kasa Ita Ce Ke Dinke Baraka Ba Kawo Rarrabuwar Kawuna Ba

by CMG Hausa
4 years ago
Kasa

Yayin taron Shangri-La, da ministocin tsaron kasashen yankin Asiya ke muhawara kan muhimman kalubalen tsaro da yankin ke fuskanta tare da gabatar da dabarun shawo kansu, sakataren tsaron Amurka Lloyd J. Austin III ya tabo wasu batutuwa da suka shafi kasar Sin.

Ya ce a baya-bayan nan, ana samun matsi daga rundunar sojin kasar Sin a yankin tekun kudancin kasar. Sai dai rahotanni sun nuna cewa, sama da jiragen ruwa 100,000 ne ke zirga-zirga a tekun a kowacce shekara, kuma babu wanda ya taba fuskantar barazana.

  • Sin Ta Gudanar Da Ayyukan Nazarin Kayan Tarihi Fiye Da 8800 A Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Tabbas kasar Sin ba ta takalar fada, sai dai mayar da martani idan aka takale ta. Don haka, duk wani wanda zai yi korafi game da fuskantar barazana daga rundunar sojin kasar Sin, to takalarta ya yi ko keta dokokin, domin Sin ba ta daukar wargi.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, ba su sauya matsayarsu kan manufar kasar Sin daya tak a duniya da yarjejeniyoyin da kasashen biyu suka cimma ba, amma kuma za su ci gaba da taimakawa Taiwan zama mai dogaro da kanta a fannin tsaron kai.

Shin me hakan ke nufi? Duk wanda ya amince da ka’idar kasancewar kasar Sin daya tak da gaske, ya san cewa bai halarta ya yi wata hulda ta kai tsaye da yankin Taiwan ba.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Ikirarin taimakawa Taiwan ta fuskar tsaro, ya nuna karara cewa, Amurka na goyon bayan masu neman ballewar yankin, abun da Sin ta sha nanata cewa ba mai yuwuwa ba ne. Kuma a matsayinta na mai wakiltar baki daya Jamhuriyar kasar Sin, batun tsaron Taiwan, hakki ne na kasar Sin, ba wata kasar waje ba.

Amurka na ikirarin ta damu da tsaron yankin Asiya. Idan har da gaske take, ganin cewa dukkan kasashen yankin na da cikakken iko da yankunansu, kamata ya yi a yi la’akari da bukatun da damuwar kowacce kasa.

Kamata ya yi a girmama ’yancin kasashen yankin da hanyoyin ci gaba ko tafiyar da mulki ko na tabbatar da tsaro da suka zabarwa kansu. Bai dace wata kasa ta yi kokarin kakkaba tsarinta a kan wata ba, domin mai daki shi ya san inda yake masa yoyo.

Har ila yau, ya ce matsayin babbar kasa na nufin daukar babbar nauyi. Sai dai sam wannan suna ba ta dace da Amurka ba. Babbar kasa ita ta san ya kamata, ita ke dinke baraka idan ta bullo, ba rura wutar rikici ba, ita ke hade kan al’umma ba kawo rarrabuwar kawuna ba. (Fa’iza Mustapha)

Kasa
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Yang Jiechi Ya Gana Da Mai Taimakawa Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaron Kasa

Yang Jiechi Ya Gana Da Mai Taimakawa Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.