ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kasa Ita Ce Ke Dinke Baraka Ba Kawo Rarrabuwar Kawuna Ba

by CMG Hausa
4 years ago
Kasa

Yayin taron Shangri-La, da ministocin tsaron kasashen yankin Asiya ke muhawara kan muhimman kalubalen tsaro da yankin ke fuskanta tare da gabatar da dabarun shawo kansu, sakataren tsaron Amurka Lloyd J. Austin III ya tabo wasu batutuwa da suka shafi kasar Sin.

Ya ce a baya-bayan nan, ana samun matsi daga rundunar sojin kasar Sin a yankin tekun kudancin kasar. Sai dai rahotanni sun nuna cewa, sama da jiragen ruwa 100,000 ne ke zirga-zirga a tekun a kowacce shekara, kuma babu wanda ya taba fuskantar barazana.

  • Sin Ta Gudanar Da Ayyukan Nazarin Kayan Tarihi Fiye Da 8800 A Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Tabbas kasar Sin ba ta takalar fada, sai dai mayar da martani idan aka takale ta. Don haka, duk wani wanda zai yi korafi game da fuskantar barazana daga rundunar sojin kasar Sin, to takalarta ya yi ko keta dokokin, domin Sin ba ta daukar wargi.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, ba su sauya matsayarsu kan manufar kasar Sin daya tak a duniya da yarjejeniyoyin da kasashen biyu suka cimma ba, amma kuma za su ci gaba da taimakawa Taiwan zama mai dogaro da kanta a fannin tsaron kai.

Shin me hakan ke nufi? Duk wanda ya amince da ka’idar kasancewar kasar Sin daya tak da gaske, ya san cewa bai halarta ya yi wata hulda ta kai tsaye da yankin Taiwan ba.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Ikirarin taimakawa Taiwan ta fuskar tsaro, ya nuna karara cewa, Amurka na goyon bayan masu neman ballewar yankin, abun da Sin ta sha nanata cewa ba mai yuwuwa ba ne. Kuma a matsayinta na mai wakiltar baki daya Jamhuriyar kasar Sin, batun tsaron Taiwan, hakki ne na kasar Sin, ba wata kasar waje ba.

Amurka na ikirarin ta damu da tsaron yankin Asiya. Idan har da gaske take, ganin cewa dukkan kasashen yankin na da cikakken iko da yankunansu, kamata ya yi a yi la’akari da bukatun da damuwar kowacce kasa.

Kamata ya yi a girmama ’yancin kasashen yankin da hanyoyin ci gaba ko tafiyar da mulki ko na tabbatar da tsaro da suka zabarwa kansu. Bai dace wata kasa ta yi kokarin kakkaba tsarinta a kan wata ba, domin mai daki shi ya san inda yake masa yoyo.

Har ila yau, ya ce matsayin babbar kasa na nufin daukar babbar nauyi. Sai dai sam wannan suna ba ta dace da Amurka ba. Babbar kasa ita ta san ya kamata, ita ke dinke baraka idan ta bullo, ba rura wutar rikici ba, ita ke hade kan al’umma ba kawo rarrabuwar kawuna ba. (Fa’iza Mustapha)

Kasa
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Yang Jiechi Ya Gana Da Mai Taimakawa Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaron Kasa

Yang Jiechi Ya Gana Da Mai Taimakawa Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.