• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Ƙara Ƙaimin Aiki, Inda Shugabanta Ya Buɗe Sabon Ofishin Ingancin Aiki

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa bisa jagorancin shugabanta, CGI Isah Jere Idris, ta ƙara matsa ƙaimin tabbatar da ingancin aikin da take yi wa al’umma a cibiyoyin mu’amalolinta da ‘yan ƙasa.

Aiki

A sakamakon wannan sabon yunƙurin, shugabanta Isah Jere ya ƙaddamar da sabon katafaren ginin sashen kula da ingancin aiki da ake wa laƙabi da “SERVCOM”.

Aiki

Da yake jawabi a yayin bikin, Isah Jere ya sanar da sabbin abubuwan da suke ɓullo da shi domin tabbatar da ingancin aikin samar da fasfo da sauran sassan ayyuka na hukumar.

LABARAI MASU NASABA

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba

Ya ƙara da cewa, “An samar da Sashen SERƁICOM na Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya don ingancin aiki mai alfanu don tabbatar da gamsuwar abokan ciniki da kuma cike giɓin da za a iya samu a tsakanin NIS da abokan hulɗarta wajen gudanar da aiki.

aiki

“Gabaɗaya dai, Serɓicom a matsayin sashe tana aiki ne bisa muradin Fadar Shugaban Kasa da Tsarin Sauƙaƙa Yin Kasuwanci, Inda NIS ta yi aiki kuma tana ci gaba da aiki sosai. Ya kasance a rubuce a tarihi cewa NIS ta zo na farko a kan tsarin sauƙaƙa Yin Kasuwanci na Shugaban Ƙasa har sau shida (bi-da-bi).

Aiki

“Gwamnati aba ce da ta shafi jama’a kuma saboda jama’a, don haka, NIS ta mayar da hankali sosai a kan ingancin hidimar da ake yi wa ‘yan ƙasa da yadda ake biyan irin waɗannan buƙatu. Cibiyoyin gwamnati wakilci ne na gwamnati a matakai daban-daban. Galibi su ne tsarin ginshiƙan gwamnati, waɗanda ke zama wurin tuntuɓar jama’a da masu zaman kansu. A kan wannan NIS ba daban ba ce, ita ma tana ciki.

  • Barazanar Kone-konen Ofisoshin INEC Ga Zaben 2023

“Bari in tabbatar muku da cewa NIS ta himmatu wajen samar da sakamakon da ya dace da bukatun al’ummarmu ta yau ta amfani da kayan aikin da take da su a hannunta. Za mu kuma yi ƙoƙari mu yi wa duk masu ruwa da tsaki hidima cikin ƙayyadaddun lokuta mafi dacewa cikin ƙwarewarmu daidai gwargwado. Don haka muna kira ga jama’a da su ba mu goyon bayan da ya dace a ƙoƙarin da muke yi na bayar da gudunmawarmu ga samun ingantacciyar Nijeriya.” Ya bayyana.

Aiki

Wakazalika, CGI Isah Jere ya hori jami’an hukumar manya da ƙananan kowa ya yi ƙoƙarin inganta ƙwarewar aiki, domin a cewarsa, babu wurin ɓuya ga raggwaye.

“Ina kira ga duk Jami’ai da su yi amfani da wannan damar don haɓaka ƙwarewar ayyukansu. Ina kuma iya sanar da dukkan Jami’anmu cewa daga yanzu, a yanzu babu wurin buya ga duk wanda yake wasa da gudanar da aiki mai inganci. Yarjejeniyar tsarin aiki da aka sake fasali, yunƙuri ne na hana ragwanci da gazawar aiki saboda ta bayar da cikakkun bayanai a kan yadda za a bi a riƙa mu’amalar aiki da hukumar, ko neman ƙarin bayani, ko gabatar da korafe-korafe da kuma yadda za a nemi gyara wani abu da aka tafka ba daidai ba.

“Ina so in yi amfani da wannan damar wajen sanar da jama’a cewa a wani bangare na kokarin tsaftace tsarin fasfo, Hukumarmu ta bullo da tsari wanda zai ba masu neman fasfo damar zabar ranar da za a dauki bayansu a cibiyoyin hukumar. Wannan zai taimaka wa masu aiki su daidaita tsarin fasfo yayin da kuma masu neman fasfo za su samu damar zaɓen ranar da suka ga ta fi kwanciyar musu a a kai.

 

“A madadin manya da ƙananan jami’an Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya, ina jinjina wa gwamnati da al’ummar Jihar Filato bisa goyon bayan da suke bai wa ma’aikatanmu tsawon shekaru. Muna mika godiya ta musamman ga mai girma gwamna bisa goyon baya irin na uban ƙasa da yake bai wa Kwanturola na jihar da kuma sauran hidima da ake wa hukumar.” Kamar yadda ya bayyana.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

October 11, 2025
Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
Tsaro

Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba

October 11, 2025
Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
Tsaro

Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara

October 11, 2025
Next Post
Buhari Ya Yi Allah Wadai Da Sace Jarirai Sabbin Haihuwa A Anambra 

Buhari Ya Yi Allah Wadai Da Sace Jarirai Sabbin Haihuwa A Anambra 

LABARAI MASU NASABA

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

October 11, 2025
Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba

Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba

October 11, 2025
Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara

Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara

October 11, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta

October 11, 2025
Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

October 11, 2025
Matasa 2 Sun Mutu Bayan Nutsewa A Rafi A Kano

Matasa 2 Sun Mutu Bayan Nutsewa A Rafi A Kano

October 11, 2025
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

October 11, 2025
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

October 11, 2025
sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

October 11, 2025
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.