• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Oyetola Ya Ciwo Bashin Biliyan 18 Bayan Da Ya Fadi Zabe, Ba Mu San Me Zai Yi Da Su Ba – Adeleke

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Al'ajabi
0
Oyetola Ya Ciwo Bashin Biliyan 18 Bayan Da Ya Fadi Zabe, Ba Mu San Me Zai Yi Da Su Ba – Adeleke
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, ya ce, tsohon gwamnan Jihar da ya bar masa kujera, Gboyega Oyetola, ya yi gaba gadi kawai ya je ya lafto bashin naira biliyan 18 jim kadan bayan da ya fadi a zaben gwaman jihar da aka gudanar a ranar 16 ga watan July na 2022. 

Gwamnan ya ce, kudaden da Oyetola ya ciwo bashinsu bayan fadinsa zabe ba su san ina ya kai ko me ya yi da su ba.

  • Gwamnatin Oyetola Ta Gadar Mana Bashin Biliyan 76 – Adeleke 

Bisa hakan, gwamnan ya ce gwamnatinsa ta gaji bashin biliyan 407.32 zuwa watan Nuwamban 2022.

Adeleke ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis sa’ilin da ke ganawa da sarakunan gargajiya na jihar Osun a Osogbo babban birnin jihar Osun ranar Alhamis.

A cewarsa, “Gwamnatina ta gaji basukan da ake bin jihar kashi-kashi har guda takwas da suka kunshi bashin albashi, tulin basukan fansho da sauransu da Gwamnatin Oyetota ta bar mana.”

Labarai Masu Nasaba

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

“Zuwa yau ana bin jihar Osun bashin biliyan N331.32.

“Idan aka hada da basukan albashi da fansho na naira biliyan 76. Basukan za su kai biliyan N407.32. Kuma har yanzu ba a tantance nawa ‘yan kwangila ke bi ba.

“Iyaka abun da ya shigo lalitar Gwamnatin jihar zuwa ranar Litinin 29 ga watan Nuwamba, kawai albashin watan Nuwamban 2022. Bayan hakan, lalitar jihar ya kasance wayam ba komai a ciki.

“A matsayina na gwamna, zan yi tambaya a madadinku. Kuma gaskiya muna bukatar amsa,” Adeleke ya fada wa sarakuna.

Ya kara da cewa, “Gwamnatin Oyetola dole ya fito ta yi bayanin bashin biliyan 331 da ta ciwo a madadin al’ummar jihar Osun me suka yi da shi da yaya suka kashe, ba tare da wani kwakkwaran aikin bunkasa jihar ba amma an ciwo tulin basuka.

“Kuma tilas ne gwamna Oyetola ya fito ya yi bayanin me ya yi da biliyan 18 da ya ciwo bashinsu bayan fadinsa a zabe ranar 16 ga watan July na 2022. Ya aka yi da su kuma ta yaya aka kashe su.

“Sannan, dole ya fito ya yi bayanin yadda aka yi jihar ya zama ana binta bashin albashin har naira biliyan 76 duk da cewa jihar ta samu kudaden Bail out na naira biliyan 50 daga wajen gwamnatin tarayya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Za Mu Bari A Ci Gaba Da Kai Hare-hare Ga Ofisoshin INEC Ba, Cewar Sufeton ‘Yansanda

Next Post

Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Fadada Kasuwannin Cikin Gida

Related

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

4 days ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

4 days ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

2 weeks ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi

2 months ago
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
Al'ajabi

Wani Jami’in Ɗansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa

3 months ago
Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja
Al'ajabi

Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja

4 months ago
Next Post
Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Fadada Kasuwannin Cikin Gida

Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Fadada Kasuwannin Cikin Gida

LABARAI MASU NASABA

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

May 10, 2025
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

May 10, 2025
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.