ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Oyetola Ya Ciwo Bashin Biliyan 18 Bayan Da Ya Fadi Zabe, Ba Mu San Me Zai Yi Da Su Ba – Adeleke

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Oyetola

Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, ya ce, tsohon gwamnan Jihar da ya bar masa kujera, Gboyega Oyetola, ya yi gaba gadi kawai ya je ya lafto bashin naira biliyan 18 jim kadan bayan da ya fadi a zaben gwaman jihar da aka gudanar a ranar 16 ga watan July na 2022. 

Gwamnan ya ce, kudaden da Oyetola ya ciwo bashinsu bayan fadinsa zabe ba su san ina ya kai ko me ya yi da su ba.

  • Gwamnatin Oyetola Ta Gadar Mana Bashin Biliyan 76 – Adeleke 

Bisa hakan, gwamnan ya ce gwamnatinsa ta gaji bashin biliyan 407.32 zuwa watan Nuwamban 2022.

ADVERTISEMENT

Adeleke ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis sa’ilin da ke ganawa da sarakunan gargajiya na jihar Osun a Osogbo babban birnin jihar Osun ranar Alhamis.

A cewarsa, “Gwamnatina ta gaji basukan da ake bin jihar kashi-kashi har guda takwas da suka kunshi bashin albashi, tulin basukan fansho da sauransu da Gwamnatin Oyetota ta bar mana.”

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ɗa Da Uwa Suka Ɗauki Hayar Wani Don Ya Kashe Mahaifinsa A Kano

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

“Zuwa yau ana bin jihar Osun bashin biliyan N331.32.

“Idan aka hada da basukan albashi da fansho na naira biliyan 76. Basukan za su kai biliyan N407.32. Kuma har yanzu ba a tantance nawa ‘yan kwangila ke bi ba.

“Iyaka abun da ya shigo lalitar Gwamnatin jihar zuwa ranar Litinin 29 ga watan Nuwamba, kawai albashin watan Nuwamban 2022. Bayan hakan, lalitar jihar ya kasance wayam ba komai a ciki.

“A matsayina na gwamna, zan yi tambaya a madadinku. Kuma gaskiya muna bukatar amsa,” Adeleke ya fada wa sarakuna.

Ya kara da cewa, “Gwamnatin Oyetola dole ya fito ta yi bayanin bashin biliyan 331 da ta ciwo a madadin al’ummar jihar Osun me suka yi da shi da yaya suka kashe, ba tare da wani kwakkwaran aikin bunkasa jihar ba amma an ciwo tulin basuka.

“Kuma tilas ne gwamna Oyetola ya fito ya yi bayanin me ya yi da biliyan 18 da ya ciwo bashinsu bayan fadinsa a zabe ranar 16 ga watan July na 2022. Ya aka yi da su kuma ta yaya aka kashe su.

“Sannan, dole ya fito ya yi bayanin yadda aka yi jihar ya zama ana binta bashin albashin har naira biliyan 76 duk da cewa jihar ta samu kudaden Bail out na naira biliyan 50 daga wajen gwamnatin tarayya.”

Oyetola
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Yadda Ɗa Da Uwa Suka Ɗauki Hayar Wani Don Ya Kashe Mahaifinsa A Kano
Al'ajabi

Yadda Ɗa Da Uwa Suka Ɗauki Hayar Wani Don Ya Kashe Mahaifinsa A Kano

August 14, 2026
Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Al'ajabi

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Next Post
Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Fadada Kasuwannin Cikin Gida

Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Fadada Kasuwannin Cikin Gida

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.