• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Kara Harajin Tallafin Bunkasa Ilimi

by Sulaiman
3 years ago
Ilimi

Gidauniyar Tattara Harajin Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFund) ta nemi a kara yawan harajin da ake karbar don tallafa wa harkar ilimin manyan makarantu zuwa kashi 3 a cikin dari. Gidauniya ta bayyana cewa, neman karin ya zama dole ne don a samu kudaden bunkasa harkar karatun manyan makarantun kasar nan yadda yakamata.

Shugabanin hukumar sun bayyana cewa, ana fuskantar matsaloli wajen cimma manufar kafar gidauniyar saboda yadda ake fuskantar matsalar tattalin arziki ba wai a Nijeriya kadai ba har ma a sauran Kasashen Afrika, inda gwamnatoci ke fafutukar farfado da hanyoyin tattara haraji ga shi kuma suna fuskantar basussukan cikin gida dana kasashen waje, kara wani haraji zai kai haifar da matsalolin ne da ba a sai iyakarsu ba.

  • Daga Asabar 8 Zuwa Talata 11 Ga Watan Muharram 1444

Yakamata a lura da cewa, gwamnatin tarayya ta kafa hukumar TETFund a shekarar 2021 ne ta zama wata kafar bayar da tallafi ga manyan makarantun kasar nan musamman ma abin da ya shafi gine-gine da samar da kayyakin aiki ga manyan makarantun a fadin tarayyar Nijeriya.

An dora harajin tallafin ilimin ne ga kanfanonin Nijeriya inda suke bayar da kashi 2.5 na ribar da suka samu a duk shekara don taimakawa sashen ilimin manyan makarantun Nijeriya.

Yana kuma da muhimmanci a sani cewa a tsakanin shekarar 1998 zuwa 2018, TEDFUND ta rarraba wa manyan makarantun kasar nan fiye da naira Tiriliyan 1, manyan makarantun sun hada da jami’o’i, Makarantar Fasaha da makarantun Kwalejojin Horar da mayan malamai, ya zuwa shekarar 2021, jimillar manyan makarantu 221 suka amfana daga tallafi daban-daban na TEDFUND sun kuma hada da Jami’o’i 87, Makarantar Fasaha 65 da makarantun Kwalejojin Horar da mayan malamai 69. Wannan namijin kokarin ne ya sa hukumar ke neman a karin harajin da take karba don karin manyan makarantu su amfana da wannan tallafin, suna neman a kara harajin akkalla zuwa kashi 0.5.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Ra’ayin wannan jaridar a nan shi ne lallai lamarin ya zama dole in aka lura da yawan yaje-yajen aikin da malaman manyan makarantu ke yi da kuma halin tabarbarewar da makarantunmu ke ciki da kuma babbar matsalar wadda take ci wa manyan makarantun tuwo a kwarya, su ne na kudaden gudanarwa da ya yi matukar karanci.

A ra’ayinmu abin takaicin shi ne yadda lamarin samar wa manyan makarantu kudaden gudanar da ayyukansu ya zama tashin hankali, wannan kuma tun daga gwamnatocin da suka gabata ne, wasu masana sun bayyana cewa, Nijeriya na bukatar akalla Naira Tiriliyan 2 don farfado da sashin ya yi daidai da takwarorinsa na kasashen duniya.
Rahoto ya nuna cewa, a tsakanin shekara 6 (2016 zuwa 2021) Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta samarwa bangaren ilimi Naira Tiriliyan 55.3, amma Naira Tiriliyan 3.5 kasa da kashi 10 kena suka samu shiga hannun bangaren.

Tabbas wannan abin takaici ne matuka, kuma bai kamata ba, hakan kuma na daga cikin korafe-korafen kungiyar Malamai ta ASUU wanda ya kai su ga shiga yajin aiki har na wata 16 tun da aka shiga tsarin mulkin dimokradiyya a kasar nan a shekarar 1999, babbar korafinsu yana tattare da batun samarwa da jami’o’in kudaden gudanarwa ne.

Masana sun bayyana cewa, gwamnatin tarayya kadai ba za ta iya samarwa manyan makarantun kudaden da suke bukata ba musamman ma ganin yadda ake fuskantar karancin kudaden shiga da kuma yadda ake fuskantar karuwar manyan makaranhtu ba tare da wani tsari ba, ana yi ne saboda biyan wasu bukatu na siyasa.

Babu tantama cewa, TETfund ta yi gaggarumin kokari wajen samarwa wasu manyan makarantu kayan aiki da gine-gine masu inganci, amma lalle akwai karin bukatar aiki sosai a bangaren. Tabbas yawancin manyan makarantunmu na fuskantar lalacewar gine-gine kamar dakunan kwanan dalibai da wuraren karatu dama hanyoyin cikin jami’o’in duki sun lalace, wasu wuraren ma ba zai yiyu a ce dandama na zama a wurin ba. Wannan ya sa ya zama dole a samar wa da manyan makarantunmu isasssun kudade ta yadda za su yi gogayya da takwarorinsu na kasashen duniya da suka cigaba.

Amma a halin yanzu ‘yan Nijeriya da dama suna nuna damuwarsu a kan yadda kananan da matsakaitun kamfanoni suke fuskantar haraji daban-daban, a wasu jihohin kamfanoni na biyan haraji daban-daban har fiye da kashi 20. Hukumar kula da tattara haraji ta bayyana cewa, a Nijeriya mutane 10,006,304 ke biyan haraji wanda ke nuna kashi 5 kenan nan ke daukar nauyin al’ummar Nijeriya da suka kai fiye da mutum miliyan 200.

A ra’ayinmu yakamata ba fadada kokakrin karbar harajin ya hada da karin mutane don kaucewa dora nauyi a kan wasu ba’adin mutane kadan, ya kuma kamata a kaucewa karbar haraji barkatai a hannun mutane.

Muna goyon bayan karin akalla kashi 3 na harajin ilimi saboda mun yi imanin hakan zai matukar taimakawa wajen maganin matsalolin da bangaren ilimin manyan makarantun Nijeriya suke fuskanta. Ya kuma kamata manyan makaratunn kasar nan su samarwa kansu salon samun kudaden shiga kamar dai yadda ake samu a kasashen Turai da Amurka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Next Post
katin zabe

Matsaloli Da Korafe-Korafe Da Suka Dabaibaye Karbar Sabon Katin Zabe

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.