• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Banda

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya ce, biyaya ga doka da oda ne kawai zai sanya ba za su shiga har cikin gidan gwamnatin jihar Bauchi su kwato mulkinsu da ya suka ya bari ba.

Adamu ya ce, tun asali jihar Bauchi da al’umarta masoya jam’iyyar APC ne, don haka ya nuna kwarin guiwarsa na cewa za su yi wa PDP tumbur a zaben 2023 da ke tafe.

  • “Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana’a Ba A Bauchi” —Sadique
  • Ina Jin Takaici Da Damuwa Kan Yadda Ake Fita Daga Jam’iyyarmu Ta APC —Abdullahi Adamu

Abdullahi Adamu wanda ya bayyana hakan a jawabin da ya gabatar ranar Alhamis lokacin bikin kaddamar da yakin neman zaben gwamna na jam’iyyar APC tare da mika tutar jam’iyyar ga Air Marshal Sadique Baba Abubakar.

An gudanar da taron a filin wasa na jihar Bauchi, taron kuma ya samu halartar dumbin jama’a daga ciki da wajen jihar.

Adamu ya ce, “Da so samu ne ni Abdullahi Adamu da zan ce ku shiga ku kwato gwamnati da karfin tsiya, to amma saboda sanin doka zamu bi doka, zamu bi ka’ida, kuma in Allah ya so ya yarda, gwamnatin nan ta jihar Bauchi zata tabbata a hannun Air Marshal Sadique Baba Abubakar,”

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

“A jihar Bauchi mun yi barin mulki, mata za su fi mu sanin bari, to mun yi barin mulki. Gwamnatin Bauchi, Gwamnatin APC ce, ko ba haka ba ne? In kuwa haka ne ya aka yi yau Mulki ba ya hannunmu? Ko me ma ya faru, cikin ikon Allah lokacin sake sabon zubi ya yi, za a yi sabon zabe.

“Ranar 25 ga watan Afrilu za a yi zaben shugaban kasa wanda dukkaninmu hankalinmu ya taru mu zabi Bola Ahmed Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya. In Muna son a yi tafiya mai riba ya kamata idan muna da shugaban kasa dan APC to a samu gwamnan Jiha dan APC.

“Mu yi wa kanmu adalci mu samu dan APC a gidan gwamnati a ofishin gwamnan Jihar Bauchi, wannan bawan Allah kuwa shi ne, Air Marshal Sadique Baba Abubakar.” Cewar Shugaban Jam’iyyar APC, Abdullahi Adamu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
Banda
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta
Siyasa

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.