ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abdullahi Adamu: Babu Wani Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Da Aka Haramta Wa Takara A APC

by yahuzajere
4 years ago
Abdullahi Adamu

Abdullahi Adamu

Abdullahi Adamu, shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, ya ce, babu wani ɗan takarar shugaban ƙasa da aka haramtawa tsayawa takara a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne kwamitin tantancewa ƙarƙashin jagorancin John Oyegun, tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa ya gabatar da rahotonsa ga shugaban jam’iyyar APC.

Oyegun ya ce, kwamitin ya fito da jerin sunayen ’yan takara 13 daga cikin 23 da suka gabatar da kansu domin tantancewa.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani
  • ‘Yan Bindiga Sunyi Garkuwa Da Mahaifiyar A.A Zaura

Da ya ke magana da manema labarai a ranar Asabar, Adamu ya ce, tantancewar tamkar jarrabawa ce da ɗalibai ke fitowa da maki daban-daban.

Rahotanni sun nuna cewa, mutum 13 da ke fatan tsayawa takarar shugaban ƙasa an kasafta su cikin jerin sunayen waɗanda Oyegun ke jagoranta, yayin da sauran goman da ke fatan shugaban ƙasa ba su shiga cikin jerin sunayen ba.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Waɗanda aka sanya a cikin jerin sune Tinubu, mataimakin shugaban ƙasa Yemi Osinbajo; Rotimi Amaechi, ministan sufuri; Ahmad Lawan, shugaban majalisar dattawa; Yahaya Bello, gwamnan Kogi; Kayode Fayemi, gwamnan Ekiti, da Emeka Nwajiuba, tsohon ƙaramin ministan ilimi.

Sauran sun haɗa da Ogbonnaya Onu, tsohon ministan kimiyya da fasaha; Ibikunle Amosun, tsohon gwamnan Ogun; David Umahi, gwamnan Ebonyi, Muhammad Badaru, gwamnan Jigawa; Godswill Akpabio, tsohon gwamnan Akwa Ibom; da Tein Jack-Rich, wani ma’aikacin mai.

Sauran ’yan takara 10 da ba a sanya su cikin jerin ba sun haɗa da Tunde Bakare, Rochas Okorocha, Ben Ayade, Sani Yerima, Ken Nnamani, Ikeobasi Mokelu, Demeji Bankole, Felix Nicholas, Uju Ken-Ohanenye, da Ajayi Borroffice.

Abdullahi Adamu dai ya mike haikan wajen ganin APC ta tsayar da dan takarar da zai samu karbuwa a wurin ‘Yan Nijeriya domin jam’iyyarsa ta ci gaba da jan ragamar mulkin Nijeriya a 2023.

Abdullahi Adamu
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Zaben Fidda Gwani: An bukaci Deliget Din APC Da Su Zabi Osinbajo

Zaben Fidda Gwani: An bukaci Deliget Din APC Da Su Zabi Osinbajo

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.