ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abdullahi Adamu: Babu Wani Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Da Aka Haramta Wa Takara A APC

by yahuzajere
4 years ago
Abdullahi Adamu

Abdullahi Adamu

Abdullahi Adamu, shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, ya ce, babu wani ɗan takarar shugaban ƙasa da aka haramtawa tsayawa takara a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne kwamitin tantancewa ƙarƙashin jagorancin John Oyegun, tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa ya gabatar da rahotonsa ga shugaban jam’iyyar APC.

Oyegun ya ce, kwamitin ya fito da jerin sunayen ’yan takara 13 daga cikin 23 da suka gabatar da kansu domin tantancewa.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani
  • ‘Yan Bindiga Sunyi Garkuwa Da Mahaifiyar A.A Zaura

Da ya ke magana da manema labarai a ranar Asabar, Adamu ya ce, tantancewar tamkar jarrabawa ce da ɗalibai ke fitowa da maki daban-daban.

Rahotanni sun nuna cewa, mutum 13 da ke fatan tsayawa takarar shugaban ƙasa an kasafta su cikin jerin sunayen waɗanda Oyegun ke jagoranta, yayin da sauran goman da ke fatan shugaban ƙasa ba su shiga cikin jerin sunayen ba.

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Waɗanda aka sanya a cikin jerin sune Tinubu, mataimakin shugaban ƙasa Yemi Osinbajo; Rotimi Amaechi, ministan sufuri; Ahmad Lawan, shugaban majalisar dattawa; Yahaya Bello, gwamnan Kogi; Kayode Fayemi, gwamnan Ekiti, da Emeka Nwajiuba, tsohon ƙaramin ministan ilimi.

Sauran sun haɗa da Ogbonnaya Onu, tsohon ministan kimiyya da fasaha; Ibikunle Amosun, tsohon gwamnan Ogun; David Umahi, gwamnan Ebonyi, Muhammad Badaru, gwamnan Jigawa; Godswill Akpabio, tsohon gwamnan Akwa Ibom; da Tein Jack-Rich, wani ma’aikacin mai.

Sauran ’yan takara 10 da ba a sanya su cikin jerin ba sun haɗa da Tunde Bakare, Rochas Okorocha, Ben Ayade, Sani Yerima, Ken Nnamani, Ikeobasi Mokelu, Demeji Bankole, Felix Nicholas, Uju Ken-Ohanenye, da Ajayi Borroffice.

Abdullahi Adamu dai ya mike haikan wajen ganin APC ta tsayar da dan takarar da zai samu karbuwa a wurin ‘Yan Nijeriya domin jam’iyyarsa ta ci gaba da jan ragamar mulkin Nijeriya a 2023.

Abdullahi Adamu
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Next Post
Zaben Fidda Gwani: An bukaci Deliget Din APC Da Su Zabi Osinbajo

Zaben Fidda Gwani: An bukaci Deliget Din APC Da Su Zabi Osinbajo

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.