• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Tube Wa Mahaifinta Rawani, Kwamishina Ta Yi Murabus A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Bayan Tube Wa Mahaifinta Rawani, Kwamishina Ta Yi Murabus A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasa da ‘yan awanni da cire mahaifinta daga sarautar Wazirin Bauchi, Kwamishiniyar ma’aikatar kasuwanci da masana’antu ta jihar Bauchi, Hajiya Sa’adatu Bello Kirfi ta yi murabus daga mukaminta. 

 

Sa’adatu a wata wasikar da ta aike wa gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad mai kwanan wata 4 ga Janairun 2023 ta ce ajiye aikin nata ya fara aiki ne nan take.

  • An Tsige Wazirin Masarautar Bauchi Kan Rashin Yi Wa Gwamna Biyayya

Daga bisani ta gode wa gwamnan Jihar a bisa ba ta damar zama daga cikin mambobin Majalisar zartaswa ta jihar.

 

Labarai Masu Nasaba

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

Duk da ya ke dai ba ta yi bayanin dalilan da suka sanya ta ajiye mukamin nata ba, ana ganin bai rasa nasaba da korar mahaifinta Alhaji Muhammad Bello Kirfi daga Sarautarsa ta Wazirin Bauchi ba bisa abun da aka misalta rashin biyayya da rashin mutunta gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad da aka sameshi da yi.

 

A wasikar tsige Bello Kirfi daga mambar Majalisar masarautar ta Bauchi mai dauke da kwanan wata Talata 3 ga watan Janairun 2023 dauke da sanya hannun sakataren masarautar, Alhaji Shehu Mudi Muhammad da wakilinmu ya ci karo da ita.

 

Wani bari na wasikar na cewa, “An umarceni da na koma ga wasikar da aka samu daga ma’aikatar kananan hukumomi da kula da harkokin masarautun gargajiya mai lamba MLG/LG/S/72/T da ke dauke da kwanan wata 30 ga watan Disamban 2022.”

 

“Wasikar na kunshe da cewa ba ka biyayya da mutunta mai girma gwamnan Jihar Bauchi da Gwamnati. Kan hakan an umarci a cire ka nan take.

 

“Bisa bayanan da suke a sama, an cireka daga ofis a matsayin Wazirin Bauchi kuma mamba a cikin Majalisar masarautar Bauchi”.

 

Alhaji Shehu Mudi Muhammad daga bisani ya yi wa korarren Wazirin Bauchi fatan alkairi a rayuwarsa ta gaba.

 

LEADERSHIP Hausa ta yi tilawar cewa shi dai Wazirin Bauchi, Alhaji Muhammad Bello Kirfi an taba dakatar da shi daga sarautarsa a zamanin mulki gwamna Muhammad Abdullahi Abubakar wanda Sarkin Bauchi Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu ya yi a watan Maris na 2017.

 

Bayan da gwamna Bala Muhammad Abdulkadir ya zama gwamna a 2019 ya shiga ya fita har aka samu nasarar sake dawowa Muhammad Bello Kirfi da Sarautarsa, yanzu kuma an koreshi gaba daya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’ajabi: Yadda Mata Da Miji Suka Rasu Akan Gadon Aurensu A Kano

Next Post

Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

Related

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

41 minutes ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

2 hours ago
Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
Labarai

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

2 hours ago
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
Labarai

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

3 hours ago
Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA
Labarai

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

4 hours ago
Next Post
Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Lardin Hainan Na Kasar Sin Ya Samu Karuwar Cinikayyar Hajoji Da Aka Daukewa Haraji Cikin Shekaru Biyar

Lardin Hainan Na Kasar Sin Ya Samu Karuwar Cinikayyar Hajoji Da Aka Daukewa Haraji Cikin Shekaru Biyar

July 4, 2025
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

July 4, 2025
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

July 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

July 4, 2025
Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

July 4, 2025
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

July 4, 2025
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

July 4, 2025
Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

July 4, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

July 4, 2025

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.