ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
hatsarin mota

Hukumar kiyaye aukuwar hadura ta kasa (FRSC) reshen jihar Bauchi ta tabbatar da cewa mutane goma sha takwas (18) ne suka kone kurmus har ma ba a iya tantance su a wani mummunar hatsarin mota da ya faru gaf da kauyen Nabardo da ke cikin karamar hukumar Toro a kan babbar hanyar Bauchi zuwa Jos. 

 

Hatsarin wanda ya kunshi motoci biyu motar kabu-kabu Toyota Hiace Bus mai lamba: FKE 688 YC da wata katuwar Tirela inda suka yi taho-mu-kara da juna.

ADVERTISEMENT
  • 15 Sun Mutu, 5 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi – FRSC 

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, Kwamandan shiyya na hukumar, Malam Yusuf Abdullahi, ya ce, hatsarin ya faru ne da yammacin ranar Laraba, ya ce mutum 21 ne hatsarin ya shafa da suka hada da manyan mutane Maza 18 da kuma yara uku.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ya nuna matukar takaicinsa bisa faruwar hatsarin duk da kokarin da suke yi ba dare ko rana wajen wayar da kan direbobi wajen ganin sun kauce wa tukin ganganci da gudun wuce kima amma sun kasa bin matakan da ake son su bi.

 

“Abun bakin ciki da takaici ne gaskiya. Kullum sai mun shafe sama da awa biyu muna wayar wa direbobi kai kan tukin wuce kima amma ina ba su ji.

 

“Yanzu ka duba wannan hatsarin da ya faru direban Bas din da dukkanin fasinjojinsa sun kone sun zama toka ba a ma iya gane kowa a cikinsu.

 

“Abun bakin cikin da ya faru da yammacin ranar Laraba mutum 18 suka mutu a mummunar hatsarin da ya faru kasa da kilomita uku zuwa kauyen Nabardo da ke kan hanyar Bauchi zuwa Jos.”

 

Ya ce, hatsarin ya faru ne sakamakon kauye wa ka’idojin tuki, “Mun fahimci cewa direban Bas din ya rasa shawo kan ikon motar ne wanda hakan ya sanya ya fita daga kan layinsa inda ya doshi inda Tirela take suka kara kuma kun san wurin ajiyar Mai na Hummer na kusa da injinta ne.

 

“Lamarin ya janyo karawa a tsakanin motocin biyu. Hatsarin kuma ya faru ne a cikin daji babu mutane a wajen balle su kai aikin gaggawa garesu. Dukkanin mutanen cikin motar ‘Bas’ da fasinjojinsa sun kone kurmus,” ya shaida.

 

Shugaban ya kara da cewa ‘yan sanda da jami’an ma’aikatar kula da walwala da jin dadi za su kula da yi musu jana’izar bai-daya.

hatsarin mota
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
NDLEA Ta Cafke Mutum 1,232 Da Miyagun Kwayoyi A Kaduna

NDLEA Ta Cafke Mutum 1,232 Da Miyagun Kwayoyi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.